Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20
Published: November 21, 2025 at 4:36 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Fadar shugaban Amurka ta White House ta musanta kalamun da shugaba Cyril Ramaphosa na Afrika Ta Kudu (ATK) yayi jiya Alhamis inda yake cewa Amurka tana tunanin canja ra’ayinta game da kauracewa taron kolin kasashen kungiyar G20 a birnin Johannesburg.

A wajen wani taron manema labarai da manyan jami’an Kungiyar Tarayyar Turai jiya alhamis, shugaba Ramaphosa yace sun samu wata sanarwa daga Amurka game da canja ra’ayi ko kuma dai halartar taron a wani matsayi.

Wata jami’ar White House ta musanta wannan, tana mai cewa karamin jakadan Amurka dake Pretoria zai je wurin taron ne domin karbar ragamar jagorancin kungiyar na karba-karba wanda zai komo hannun Amurka, amma ba wai don halartar wani abu na taron ba.

Gwamnatin shugaba Trump ta ce Amurka ba zata halarci taron farko na kungiyar G20 da za a yi a Afirka ba, tana mai zargin cewa ATK mai masaukin baki, wadda turawa ‘yan tsiraru na kasar suka mulke ta har zuwa 1994, tana gallazawa da cin mutuncin turawan kasar.

Ita dai kungiyar ta G20, kungiya ce ta kasashe 19 da suka kunshi wadanda suka fi arziki da kuma wadanda tattalin arzikinsu ke tasowa sosai. A shekarar 2023, KTT da KTA, sun shiga a zaman membobi masu wakiltar kasashensu, kungiyar ta zamo mai membobi 21.

Wannan kungiya, ba kamar kungiyar G7 ta kasashe mafiya arziki zalla ba, tana mayarda hankulanta ne kan tattalin arzikin duniya da ayyukan raya kasa. Sai dai kungiyar ba ta da hedkwata, kuma ba ta cimma shawarwarin da dole membobi suyi aiki da su, abinda ya sa masu sukar lamiri suke ce kungiyar haushi kawai ta iya, ba ta da hakoran yin cizo.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025
Next Post: Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
Habasha Tafara Gina Filin Jirgin Sama Mafi Girma A Afirka Afrika
Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa Afrika
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
  • ‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
  • Rasha: Zamu Ba Gwamnatin Venezuel Gudunmawa Sauran Duniya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.