Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa
Published: November 29, 2025 at 8:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 29, 2025

Kamfanin Orano ya sanar cewa hukumomn Nijar sun fara aiyukan fitar da ton ton na Uranium daga garin Arlit zuwa waje ba tare da sanar da shi ba. Matakin da kamfanin na Faransa ya ce ya saba wa umurnin kotun bankin duniya, wace ta bukaci bangarorin su jira ta kammala shari’ar da ke gabanta.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnatin Nijar  sai dai kwararru kan sha’anin ma’adanai sun fara bayyana matsayinsu.
A kalla ton 1300 na Uranium ne ke jibge a kamfanin SOMAIR da ke Arlit na arewacin Nijar bayan da gwamnatin kasar ta dakatar da fitarwa zuwa waje a washegarin juyin mulkin Yulin 2023, saboda abin da suka kira rashin haske daga kamfanin Orano da ke harkar Uranium shekaru sama da 50.
Dangantaka ta ci gaba da tsami a tsakanin bangarorin biyu abin da ya sa Orano shigar da kara a kotun CIRDI domin ta shiga tsakani. A yayin da ake jiran matsayin kotun kamfanin na Faransa ya sanar cewa motoci dauke da lodin Uranium sun fara dagawa daga Arlit zuwa Agadez a yunkurin Isa gabar teku. Kwararre kan sha’anin albarkatun karkashin kasa Mahamadou Tchiroma Aissami na fassara abin a matsayin ci gaban takaddama.
Kamfanin na Orano ya ce fitar da Uranium a wannan lokaci ya saba wa umurnin kotu. sai dai ‘yan Nijar irinsu masani a harakar makamashi injiniya Rabiou Malan Issa na ganin koma mai ake ciki Nijar ce uwar gijiyar albarkatun da ake rikicin kan su.
 Nijar na daga cikin kasashen da suka rattaba hannu kan yarjeniyoyin hakar ma’adanai da hanyoyin sayar da su a kasuwannin duniya, dalili kenan wadanda suka lakanci fannin ke gargadin mahukunta a kan hanyoyin mafita.
 Jamhuriyar Nijar na daga cikin kasashen da suka fi kowa yawan Uranium a duniya sai dai alamu na nunin kasar da al’ummarta ba su amfana da arzikin, kamar yadda ya dace abin da ya sa gwamnatin CNSP ta dage da yunkurin sabunta abokan hulda a wannan fanni kuma bayanai na cewa kamfanin ROSATOM na Russia na daga cikin masu fatan ganin an ba su dama.
Afrika

Post navigation

Previous Post: Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed
Next Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!

Karin Labarai Masu Alaka

Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata Afrika
Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika
Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado Afrika
Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
  • Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon Wasanni
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.