Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa
Published: November 29, 2025 at 8:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 29, 2025

Kamfanin Orano ya sanar cewa hukumomn Nijar sun fara aiyukan fitar da ton ton na Uranium daga garin Arlit zuwa waje ba tare da sanar da shi ba. Matakin da kamfanin na Faransa ya ce ya saba wa umurnin kotun bankin duniya, wace ta bukaci bangarorin su jira ta kammala shari’ar da ke gabanta.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnatin Nijar  sai dai kwararru kan sha’anin ma’adanai sun fara bayyana matsayinsu.
A kalla ton 1300 na Uranium ne ke jibge a kamfanin SOMAIR da ke Arlit na arewacin Nijar bayan da gwamnatin kasar ta dakatar da fitarwa zuwa waje a washegarin juyin mulkin Yulin 2023, saboda abin da suka kira rashin haske daga kamfanin Orano da ke harkar Uranium shekaru sama da 50.
Dangantaka ta ci gaba da tsami a tsakanin bangarorin biyu abin da ya sa Orano shigar da kara a kotun CIRDI domin ta shiga tsakani. A yayin da ake jiran matsayin kotun kamfanin na Faransa ya sanar cewa motoci dauke da lodin Uranium sun fara dagawa daga Arlit zuwa Agadez a yunkurin Isa gabar teku. Kwararre kan sha’anin albarkatun karkashin kasa Mahamadou Tchiroma Aissami na fassara abin a matsayin ci gaban takaddama.
Kamfanin na Orano ya ce fitar da Uranium a wannan lokaci ya saba wa umurnin kotu. sai dai ‘yan Nijar irinsu masani a harakar makamashi injiniya Rabiou Malan Issa na ganin koma mai ake ciki Nijar ce uwar gijiyar albarkatun da ake rikicin kan su.
 Nijar na daga cikin kasashen da suka rattaba hannu kan yarjeniyoyin hakar ma’adanai da hanyoyin sayar da su a kasuwannin duniya, dalili kenan wadanda suka lakanci fannin ke gargadin mahukunta a kan hanyoyin mafita.
 Jamhuriyar Nijar na daga cikin kasashen da suka fi kowa yawan Uranium a duniya sai dai alamu na nunin kasar da al’ummarta ba su amfana da arzikin, kamar yadda ya dace abin da ya sa gwamnatin CNSP ta dage da yunkurin sabunta abokan hulda a wannan fanni kuma bayanai na cewa kamfanin ROSATOM na Russia na daga cikin masu fatan ganin an ba su dama.
Afrika

Post navigation

Previous Post: Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed
Next Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!

Karin Labarai Masu Alaka

Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
  • Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
  • Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa Wasanni
  • Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
  • Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai Labarai
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.