Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya
Published: January 13, 2026 at 12:45 PM | By: Mustapha Nasiru Batsari | Updated: January 13, 2026

Bayan shafe makonni bakwai suna hutun dole, daliban makarantun firamare da sakandare a jahar filato sun koma azuzuwa don ci gaba da neman ilimi.

Rufe makarantun da gwamnatin jahar Filato ta yi a watan Nuwamban bara, ta ce ta yi ne don yin rigakafi, sakamakon matsalolin tsaro da garkuwa da dalibai da ‘yan bindiga suka yi a wassu jihohin Najeriya,
Wassu daliban firamare na makarantar gwamnati ta Obasanjo Model School dake Jos, Favour Francis Daniel da Yane Iliya Bulus Choji sun bayyana yadda zasu tinkari jarabawa bayan dawowarsu daga hutun dole.

Shugaban sashen makarantar Obasanjo Model School Jos, Mangai Obi Maren yace yayi farinciki da daliban suka dawo a ranar farko.

Da shike tun farko gwamnati ta rufe makarantun ne saboda tsaro, na garzaya ofishin shirin samadda tsaro a makarantun jahar Filato.

Daraktan tsare-tsare na shirin, Mr Ben Chikan yace gwamnati ta hada kai da masu ruwa da tsaki don samadda tsaro a makarantun jahar.
Sakatare a hukumar ilimin bai daya matakin farko a jahar Filato, Tang’an Emmanuel yace ya zaga makarantun ya kuma ga yadda malamai da dalibai suka dukufa wajen koyo da koyarwa.

Jihohi tara ne a fadin Najeriya suka rufe makarantu a watan Nuwamban dubu biyu da ishirin da biyar, yayinda gwamnatin tarayya ta rufe makarantun unity arba’in da bakwai a fadin kasar, wanda a yanzu kudan dukkan jihohin sun umurci dalibai su koma makarantu, in banda jahar Edo da ita ma ta umurci makarantun su kasance a rufe saboda matsalolin tsaro.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/DALIBAI-SUN-KOMA-MAKARANTU-1.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe
Next Post: Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Dr. Zainab Gwamna Ta Hada Mata Fiye Da 6,000 Domin Haɗin Kai Da Ci Gaba A Gombe Najeriya
Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
Shugaba Tinubu Zai Shafe Makonni Uku A Hutun Shekara-Shekara Afrika
Gombe Ta Ƙarfafa Ilimin Almajirai Da Tsangaya Don Rage Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
  • Gwamna Abba Ya Gana Da Kwankwaso Kamun Ganawarsa Da Tinubu Siyasa
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika
  • Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.