Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya
Published: January 13, 2026 at 12:45 PM | By: Mustapha Nasiru Batsari | Updated: January 13, 2026

Bayan shafe makonni bakwai suna hutun dole, daliban makarantun firamare da sakandare a jahar filato sun koma azuzuwa don ci gaba da neman ilimi.

Rufe makarantun da gwamnatin jahar Filato ta yi a watan Nuwamban bara, ta ce ta yi ne don yin rigakafi, sakamakon matsalolin tsaro da garkuwa da dalibai da ‘yan bindiga suka yi a wassu jihohin Najeriya,
Wassu daliban firamare na makarantar gwamnati ta Obasanjo Model School dake Jos, Favour Francis Daniel da Yane Iliya Bulus Choji sun bayyana yadda zasu tinkari jarabawa bayan dawowarsu daga hutun dole.

Shugaban sashen makarantar Obasanjo Model School Jos, Mangai Obi Maren yace yayi farinciki da daliban suka dawo a ranar farko.

Da shike tun farko gwamnati ta rufe makarantun ne saboda tsaro, na garzaya ofishin shirin samadda tsaro a makarantun jahar Filato.

Daraktan tsare-tsare na shirin, Mr Ben Chikan yace gwamnati ta hada kai da masu ruwa da tsaki don samadda tsaro a makarantun jahar.
Sakatare a hukumar ilimin bai daya matakin farko a jahar Filato, Tang’an Emmanuel yace ya zaga makarantun ya kuma ga yadda malamai da dalibai suka dukufa wajen koyo da koyarwa.

Jihohi tara ne a fadin Najeriya suka rufe makarantu a watan Nuwamban dubu biyu da ishirin da biyar, yayinda gwamnatin tarayya ta rufe makarantun unity arba’in da bakwai a fadin kasar, wanda a yanzu kudan dukkan jihohin sun umurci dalibai su koma makarantu, in banda jahar Edo da ita ma ta umurci makarantun su kasance a rufe saboda matsalolin tsaro.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/DALIBAI-SUN-KOMA-MAKARANTU-1.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe
Next Post: Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai

Karin Labarai Masu Alaka

Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
  • An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.