Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus
Published: April 3, 2026 at 7:21 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya

Jam’iiyyar ADC Ta Bukaci A Sauke Shugaban Hukumar Zaben Najeriya Amupitan

Gamayyar adawa ta jam’iyyar ADC ta bukaci murabus ko a sauke shugaban hukumar zaben Najeriya INEC Joash Amupitan da kwamishinoninsa daga mukaminsu don ba su da kwarin guiwar za su gudanar da zabe mai adalci.

Bukatar ta fito ne a taron gaggawa na manyan ‘yan adawar karkashin jagoransu tsohon shugaban majalisar dattawa David Mark.

“mu na bukatar murabus ko a sauke shugaban hukumar zabe da kwamishinoninsa don ba mu amince za su iya yi ma na adalci a babban zaben 2027 ba” Inji shugaban hadakar David Mark wanda ke martani mai zafi bayan matakin INEC na dakatar da amincewa da bangarori biyu masu da’awar hakkin shugabancin jam’iyyar.

INEC ta ce ta bi umurnin kotu ne wajen dakatar da karbar bayanai daga shugaban hadakar David Mark da kuma na bangaren turjiya Nafiu Bala sai an samu sabon umurnin kotu.

Mark ya ce ya kamata INEC ta jira sai kotun daukaka kara ta yi matsaya kan takaddamar, amma maimakon haka sai INEC ta bi muradun jam’iyyar APC mai mulki.

A nan Mark ya ce sun sanar da INEC gudanar da tarukan jam’iyya daga 9 ga watan nan na Afrilu inda zai karkare da babban taro ranar 14 ga wata, kuma za su cigaba da wannan shiri ba fashi.

Babban jigon hadakar tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya ce su na son lallai INEC ta yi adalci.

Ita ma shugabar mata ta jam’iyyar Na’omi Abel ta ce akwai kalubale ga hanyar da ta ce an dauka ta maida Najeriya kasa mai bin jam’iyya daya.

In za a tuna shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa ba ta sha’awar maida Najeriya kasa mai bin jam’iyyar daya.

A babban taron jam’iyyarsa ta APC, shugaba Tinubu ya ce ya yi amanna da tsarin gasa a harkokin dimokradiyya.

Za a zuba ido kan kotu da hukumar zabe don ganin ko akwai sauyin da za a iya samu yayin da kulle-kulle ko rashin jituwa ya jefa sufana a tayar ADC.

Wannan ba ma abun mamaki ba ne, don APC ma ta sha da kyar kan hatta sunanta gabanin zaben 2015 zamanin mulkin tsohon shugaba Jonathan da tsohon shugaban hukumar zabe Farfesa Attahiru Jega.

 

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/ADC-VOWS-TO-GO-AHEAD-WITH-CONGRESSES-CALL-ON-AMUPITANS-SACK.mp3

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe
Next Post: Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta Afrika
Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Aikin Kwamitin Sayar Da Kaddarorin Gwamnati Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Ya Koma Jam’iyar APM Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
  • ‘Yan Jaridar Gidan Gwamnatin Bauchi Sun Kammala Taron Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani Afrika
  • Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.