Kasashe da dama na neman hanyar da za’a bi su ci gaba da zirga-zirgar dakon makamashi ta mashigin ruwa na Hormuz a jiya Alhamis, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya dau alwashin ci gaba da kaiwa Iran hare-hare masu tsanani, abinda ya jawo farashin mai ya kara tashi, kuma ya kawo matsi ga al’umma.
A wani jawabi da yayi ranar Laraba, Trump yace za’a tsaurara kai hare-hare, kuma bai bada lokacin da za’a tsagaita yakin ba. Fadar gwamnatin Tehran ta yi barazanar mai da martani, abinda ya jawo asara a kasuwannin hannun jari.
Kasar Birtaniya ta gana da wasu kasashe 40 a jiya Alhamis ta hanyar video domin tattaunawa kan yadda za’a samu jirage su ci gaba da wucewa ta mashigin ruwa na Hormuz ba tare da takura ba, ba kuma tare da an yi wata yarjejeniya ba.


