Fafaroma Leo zai ziyarci kasashe hudu a fadin Afirka daga ranar 13 zuwa 23 ga Afrilu, fadar Vatican ta sanar a ranar Laraba, inda Fafaroma ya yi ziyararsa ta farko zuwa ketare a shekarar 2026 zuwa nahiyar da cocin Katolika ke ci gaba da bunkasa.
Fafaroma zai kuma kai ziyarar kwana guda a ranar 28 ga Maris a birnin Monaco, karamar hukumar da ke gabar tekun Faransa, kuma zai ziyarci Spain daga ranakun 6-12 ga watan Yuni, in ji fadar Vatican.
Kasashen da zai ziyar ta A Afirka, sun hada da Algeria, Angola, Equatorial Guinea da Kamaru. Ana sa ran zai jawo dimbin jama’a, ya bukaci shugabannin kasashen duniya da su goyi bayan ci gaba a nahiyar, da kuma bayyana kokarin da ake yi a tattaunawar Katolika da Musulmi.
Leo, wanda aka zaba a watan Mayu domin ya gaji marigayi Fafaroma Francis a matsayin shugaban cocin mai mutane biliyan 1.4, ya yi balaguro daya kacal zuwa ketare ya zuwa yanzu, inda ya ziyarci Turkiyya da Lebanon a watan Nuwamba da Disamba a ziyarar da aka shirya wa Francis.


