Hukumar kula da aikin Hajji ta Najeriya (NAHCON), ta ce a ranar 3 ga watan Mayun shekarar 2026 ne za a fara jigilar maniyyata daga Najeriya zuwa Kasar Saudiyya, domin gudanar da ibadar aikin Hajjin bana.
NAHCON ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktan Yaɗa Labarai, Fatima Sanda Usara, ta fitar, inda ta ce jirgin farko na kamfanin FlyNas zai tashi daga sabon filin jirgin sama na Kasa-da-Kasa na Gateway da ke Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.
Baya ga jihar Ogun, sauran jiragen da za su tashi a wannan rana sun haɗa da Kamfanonin Umza da Max Air, da za su kwashe maniyyatan jihohin Kogi da Nasarawa daga Abuja, sai Kamfanin Air Peace da zai kwashe maniyyatan jihar Oyo daga Legas.
Kazalika daga Birnin Kebbi, wani jirgin na FlyNas zai tashi da maniyyatan Jihar Kebbi.
Tuni jami’an NAHCON da suka haɗar da tawagar likitoci suka sauka a ƙasar Saudi Arabiya a ranar Talata, 28 ga watan Afrilu, domin yin shirye-shiryen tarɓar maniyyatan Najeriya.


