Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
Published: June 14, 2026 at 6:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana alhininsa kan rasuwar tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar, wanda ya rasu yayin da yake tsare a hannun masu garkuwa da mutane a Jihar Katsina.

A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce ya kadu da labarin rasuwar tsohon jami’in sojin, wanda ya yi wa ƙasa hidima na tsawon shekaru kafin ya yi ritaya.

Shugaban ƙasar ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin, musamman ga matarsa da har yanzu take hannun masu garkuwa da mutanen.

Haka kuma, ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Katsina da rundunar sojojin Najeriya bisa wannan babban rashi.

Tinubu ya jaddada cewa gwamnatin tarayya ba za ta taɓa amincewa da buƙatar ’yan ta’adda ta sakin wasu daga cikin mambobinsu da hukumomin tsaro ke tsare da su ba.

Ya tunatar da kalamansa da ya yi a ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, inda ya yi kira ga ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da masu ɗaukar nauyin ta’addanci da su miƙa wuya ko kuma su fuskanci cikakken ƙarfin gwamnatin Najeriya.

A cewarsa, “A matsayinmu na ’yan Najeriya, dole ne mu kasance cikin haɗin kai tare da tabbatar wa kanmu cewa makiyan ƙasa za su zama tarihi nan gaba kaɗan. Za mu yi nasara a kan ta’addanci tare da ci gaba da gina ƙasa mai ci gaba da wadata.”

Shugaban ƙasar ya bayyana cewa rasuwar Janar Abubakar ya kamata ta zama wani muhimmin darasi a yaƙin da ake yi da ta’addanci da masu tayar da ƙayar baya, yana mai cewa bai kamata gwamnati ta shiga wata tattaunawa ko sulhu da su ba, domin su ne manyan maƙiyan ƙasar da ya wajaba a ci gaba da murƙushewa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
Next Post: Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a Sauran Duniya
Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Tsaurara Tsaro Yayin Da Tehran Ke Shirin Karɓar Masu Jimamin Ayatollah Khamenei Afrika
Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
  • Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro Afrika
  • Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.