Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika

Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
Published: June 14, 2026 at 6:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana alhininsa kan rasuwar tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar, wanda ya rasu yayin da yake tsare a hannun masu garkuwa da mutane a Jihar Katsina.

A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce ya kadu da labarin rasuwar tsohon jami’in sojin, wanda ya yi wa ƙasa hidima na tsawon shekaru kafin ya yi ritaya.

Shugaban ƙasar ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin, musamman ga matarsa da har yanzu take hannun masu garkuwa da mutanen.

Haka kuma, ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Katsina da rundunar sojojin Najeriya bisa wannan babban rashi.

Tinubu ya jaddada cewa gwamnatin tarayya ba za ta taɓa amincewa da buƙatar ’yan ta’adda ta sakin wasu daga cikin mambobinsu da hukumomin tsaro ke tsare da su ba.

Ya tunatar da kalamansa da ya yi a ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, inda ya yi kira ga ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da masu ɗaukar nauyin ta’addanci da su miƙa wuya ko kuma su fuskanci cikakken ƙarfin gwamnatin Najeriya.

A cewarsa, “A matsayinmu na ’yan Najeriya, dole ne mu kasance cikin haɗin kai tare da tabbatar wa kanmu cewa makiyan ƙasa za su zama tarihi nan gaba kaɗan. Za mu yi nasara a kan ta’addanci tare da ci gaba da gina ƙasa mai ci gaba da wadata.”

Shugaban ƙasar ya bayyana cewa rasuwar Janar Abubakar ya kamata ta zama wani muhimmin darasi a yaƙin da ake yi da ta’addanci da masu tayar da ƙayar baya, yana mai cewa bai kamata gwamnati ta shiga wata tattaunawa ko sulhu da su ba, domin su ne manyan maƙiyan ƙasar da ya wajaba a ci gaba da murƙushewa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyoyi Sunyi Hasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka Afrika
Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
Venezuela Ta Sako Karin Mutanen Da Take Tsare Dasu Labarai
Asusun IMF Zasu Ziyarci Kasar Gabon Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
  • Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
  • Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tura Mutane 386 Gidan Yari Afrika
  • Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.