Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
Published: June 14, 2026 at 6:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana alhininsa kan rasuwar tsohon Manjo Janar Rabe Abubakar, wanda ya rasu yayin da yake tsare a hannun masu garkuwa da mutane a Jihar Katsina.

A cikin wata sanarwa da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, Tinubu ya ce ya kadu da labarin rasuwar tsohon jami’in sojin, wanda ya yi wa ƙasa hidima na tsawon shekaru kafin ya yi ritaya.

Shugaban ƙasar ya miƙa sakon ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin, musamman ga matarsa da har yanzu take hannun masu garkuwa da mutanen.

Haka kuma, ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Katsina da rundunar sojojin Najeriya bisa wannan babban rashi.

Tinubu ya jaddada cewa gwamnatin tarayya ba za ta taɓa amincewa da buƙatar ’yan ta’adda ta sakin wasu daga cikin mambobinsu da hukumomin tsaro ke tsare da su ba.

Ya tunatar da kalamansa da ya yi a ranar Dimokuraɗiyya ta 12 ga Yuni, inda ya yi kira ga ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da masu ɗaukar nauyin ta’addanci da su miƙa wuya ko kuma su fuskanci cikakken ƙarfin gwamnatin Najeriya.

A cewarsa, “A matsayinmu na ’yan Najeriya, dole ne mu kasance cikin haɗin kai tare da tabbatar wa kanmu cewa makiyan ƙasa za su zama tarihi nan gaba kaɗan. Za mu yi nasara a kan ta’addanci tare da ci gaba da gina ƙasa mai ci gaba da wadata.”

Shugaban ƙasar ya bayyana cewa rasuwar Janar Abubakar ya kamata ta zama wani muhimmin darasi a yaƙin da ake yi da ta’addanci da masu tayar da ƙayar baya, yana mai cewa bai kamata gwamnati ta shiga wata tattaunawa ko sulhu da su ba, domin su ne manyan maƙiyan ƙasar da ya wajaba a ci gaba da murƙushewa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
Next Post: Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Anfara Kirga Kuri’a A zaben Kasar Guinea Labarai
Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar-Ta-Baci A Fannin Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
  • Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Wani Jirgin Sama Ya Karya Dokar Hana Zirga Zirga Amurka
  • Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
  • Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.