Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato
Published: December 18, 2025 at 6:17 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A kalla mutane 12 suka rasa rayukan su, yayin da kuma aka yi garkuwa da wasu 3, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai farmaki wajen hakar ma’adanai a kauyen Atoso da ke jihar filato a Nijeriya, a cewar wani wakilin cikin gida ranar Laraba.

Daylop Solomon Mwantiri, wanda shi ne shugaban kungiyar matasan Berom, na Berom Youth Moulders Association (BYM), ya ce maharan, wanda ‘yan gari suka ce Fulani ne, dauke da makamai, sun kai farmakin ne a Daren Talata, inda suka jikkata karin wasu mutane biyar, da a yanzu ke kwance a Gadon asibiti da raunukan harsashin bindiga.

Wannan hari na baya bayannan nan, ya kara kunnan wutar rashin zaman lafiya da ake ta fama da shi a filato, yankin Nijeriya ta tsakiya inda yawan rigingimu na kabilanci da addini ke ta’azzara fada tsakanin manoma da makiyaya kuma ana ci gaba da samun barkewar rikici, duk da alwashin da gwamnati ta dauka na kawo zaman lafiya.

Mwantiri ya ce, harin da aka kai ranar Talata, ya biyo kwanaki kadan bayan hallaka wasu yara hudu a wani kauyen dake makwaftaka da Atoso, inda ya ke zargin hukumomi da nuna halin ko in kula.

Kungiyar ta BMY ta bukaci gwamnati da ta Aike da dakaru don su hana kiwon dabbobi a gonaki, kuma su kubuto da mutanen da aka sace.

Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai

Karin Labarai Masu Alaka

Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
An Zargi Shugaba Trump Da Kalaman Da Basu Dace Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
  • Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
  • A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • Matasa Sun Sayawa Ferfesa Pantami Fom Din Takarar Gwamnan Gombe Afrika
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.