Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
Published: July 2, 2026 at 7:08 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci masu ruwa da tsaki a kamfanonin ɗab’i na Nijeriya da su rungumi haɗin kai, sasanci da haɗin gwiwa domin bunƙasa masana’antar tare da ƙara mata ƙarfin gogayya a matakin duniya.

Ministan ya yi wannan kiran ne a ranar Talata a wurin Babban Taron Masu Ruwa da Tsaki na Maɗaba’u na Nijeriya na shekarar 2026, wanda aka gudanar a otal ɗin Nicon Luxury da ke Abuja.

A cewar sa, warware rikicin shugabanci da ya daɗe a Cibiyar Ƙwararrun Maɗaba’u ta Nijeriya (CIPPON) ya samar da wata dama ta sake farfaɗo da masana’antar da kuma amfani da cikakkiyar damar tattalin arzikin ta.

Ya ce: “Tarihi ya ba ku dama ta sake gina wannan masana’anta. Don Allah ku yi amfani da ita, ku yi aiki tare, kuma kowa ya mara wa shugabanci baya domin ku ciyar da wannan sana’a gaba tare.”

Idris ya ce rikicin da ya daɗe yana addabar cibiyar yana daga cikin batutuwan farko da aka gabatar masa bayan ya kama aiki a matsayin minista, inda ya ƙara da cewa ya zaɓi sasanci da tattaunawa ne saboda ya yi imanin cewa hakan ya fi amfani fiye da doguwar shari’a.

Ya bayyana masana’antar ɗab’i a matsayin wata muhimmiyar hanya ta bunƙasa tattalin arziki da samar da ayyukan yi, yana mai cewa idan masu ruwa da tsaki suka kasance tsintsiya maɗaurin ki ɗaya, masana’antar za ta fi samun goyon bayan gwamnati da manufofin da za su bunƙasa ta.

Ministan ya kuma tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da aiki tare da CIPPON da sauran hukumomin da abin ya shafa domin ƙarfafa ƙa’idojin ƙwarewa, inganta yanayin gudanar da sana’ar da kuma ƙara gudunmawar masana’antar wajen cigaban ƙasa.

Haka kuma ya buƙaci shugabannin cibiyar da su bai wa kowa dama ba tare da la’akari da saɓanin da ya gabata ba, yana mai cewa shugabanci mai haɗa kowa ne zai samar da zaman lafiya mai ɗorewa da kuma kyakkyawan gado ga waɗanda za su zo nan gaba.

Ya kuma shawarci masu sana’ar ɗab’i da su rungumi sababbin fasahohi domin ci gaba da kasancewa masu tasiri a wannan zamani na fasahar dijital.

A nasa jawabin, Shugaban CIPPON kuma Shugaban Majalisar Gudanarwar ta, Koko T. Clement, ya ce cibiyar ta samu cigaba tun bayan rantsar da sabuwar majalisar gudanarwar ta a watan Disamba 2025.

Ya ce sun gudanar da tattaunawa da hukumomin gwamnati domin ƙarfafa ƙa’idojin ƙwarewar sana’a, inganta tsarin tafiyar da masana’antar da kuma samar da manufofin da za su taimaka wajen bunƙasa masana’antar ɗab’i a Nijeriya.

Ya ce: “Duk abin da muke yi domin cigaban wannan cibiya ne, domin amfanin kowane mai bugu, kowane ƙwararren mai aikin marufi, kuma kowane ɗan Nijeriya da ke dogaro da wannan masana’anta. Muna kira ga duk masu ruwa da tsaki da su yi aiki tare cikin zaman lafiya da fahimtar juna domin abin da ya haɗa mu ya kasance mafi girma fiye da duk wani abin da zai raba mu.”

Taron ya samu halartar shugabannin masana’antar ɗab’i, jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki, ciki har da Magatakardan CIPPON, Malam Abubakar Ndagi; Babban Jami’in Gudanarwa na KA2 Press Limited, Injiniya Michael Akinola; Daraktan Gudanarwa na kamfanin, Mista Ademola Kasumu da manyan jami’an Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, tare da sauran masu ruwa da tsaki daga masana’antar ɗab’i.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
Next Post: Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Da Iran Sun Cimma Yarjejeniya Tsagaita Wuta Na Makonni Afrika
Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.