Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka
Published: January 28, 2026 at 11:35 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A kalla mutane 38 a jihohin Amurka 14 ne suka rasa rayukansu zuwa ranar Talata sakamakon yanayin sanyi mai tsanani da ya lullube yawancin tsakiya da gabashin kasar da dusar kankara, tare da daskararriyar kankara, a cewar jami’ai da kuma rahotanni daga kafofin yada labarai.

Yanayin tsananin sanyin ya fara ne ranar Juma’a, inda ya jibge dusar kankara a fadin sashe me girma na kasar, a karshen mako. Dusar kankarar ta jawo tsaikon zirga zirgar ababen hawan titi, kuma ta jawo An soke tashin jiragen sama. Ta kuma haifar da daukewar wutar lantarki, kafin ta lafa ranar Litinin, inda ta bar sanyi da ake ganin zai dade.

Zuwa ranar Talata, birane sun fara harhado kan masu bada agaji, domin tabbatar da cewa mazauna, musamman ma marasa matsuguni basa cikin matsala, a yayin da fiye da gidaje 550,000 da wuraren kasuwanci ke fama da rashin wutar lantarki a fadin kasar.

Cikin mutanen da suka rasa rayukan su, goma sun fito daga birnin New York, inda sanyi yayi tsananin da bai taba yi ba cikin shekaru 8, a cewar magajin gari Zohran Mamdani a wani taro na manema labarai ranar Talata, lokacin da yanayin sanyi ya kai digiri 8 a ma’aunin fahrenheit.

Duk da cewa mamatan 10 an same su ne a waje, ba’a samu damar tantancewa ko basu da matsuguni ne ba. Mamdani ya shaidawa Manema labarai ranar Litinin cewa wasu daga cikin mamatan sun yi alaka da wuraren bada mafaka a da, amma yayi wuri ace za’a fayyace abinda ya haddasa mutuwar tasu.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya
Next Post: ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya Amurka
Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
  • Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.