Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
Published: January 15, 2026 at 4:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka ta fara janye wasu ma’aikata daga sansanonin sojanta a yankin gabas ta tsakiya, a bayan da wani babban jami’in Iran ya gargadi makwabtansu cewa Iran zata kai hari kan sansanonin Amurka idan har aka kai mata hari.

A yayin da hukumomi a birnin Teheran ke kokarin kwantar da wutar tarzoma mafi muni tun bayan juyin juya halin Islama da aka yi, Teheran tana son yin hannunka mai sanda ma shugaba Donald Trump da barazanarsa ta tsoma baki domin goyon bayan masu zanga zangar kin jinin gwamnati.

Wani jami’in Amurka da bai so a fadi sunansa ba yace Amurka tana kwashe ma’aikata daga wasu muhimman sansanoninta a saboda karuwar tankiya.

Wani jami’in soja a kasar yammaci yace a bisa dukkan alamu Amurka ta yanke shawarar zata kai ma kasar Iran farmaki, amma kuma yace irin wannan dabi’a gwamnatin Trump ta saba nunawa na haddasa yanayin kokwanto a kan zata kai ne ko ba zata kai harin ba.

Amma kuma a fadarsa ta White House, shugaba Trump ya nuna alamun kamar yana jira ya ga yadda lamarin zai wakana ne, trump yace wata majiya mai tushe ta fada masa cewa yawan kashe kashe ya ragu, kuma babu wani shirin da aka yi a yanzu na zartas da hukumcin kisa a kan mutane masu yawa.

Wasu jami’an Turai guda biyu ma sun ce watakila nan da sa’o’i 24 Amurka zata kai hari a kan kasar Iran haka ma wani jami’in gwamnatin bani Isra’ila yace da ala mun shugaba Trump ya yanke shawarar zai tsoma hannu a Iran, amma ba a san irin farmakin da zai kai ko kuma lokacin kaiwa ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland
Next Post: Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato

Karin Labarai Masu Alaka

Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa Amurka
Trump: Isra’ila Ta Daina Kai Hari Ga Duk Cibiyar Iskar Gas Afrika
Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tafara Yiwa Kasar Iraq Barazana Amurka
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Hukumar Kare Hakkin ‘Yan Jarida Tace Isra’ila Ce Ta Kashe ‘Yan Jarida Kashi Biyu Bisa Uku Labarai
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.