Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya
Published: January 15, 2026 at 4:15 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka ta fara janye wasu ma’aikata daga sansanonin sojanta a yankin gabas ta tsakiya, a bayan da wani babban jami’in Iran ya gargadi makwabtansu cewa Iran zata kai hari kan sansanonin Amurka idan har aka kai mata hari.

A yayin da hukumomi a birnin Teheran ke kokarin kwantar da wutar tarzoma mafi muni tun bayan juyin juya halin Islama da aka yi, Teheran tana son yin hannunka mai sanda ma shugaba Donald Trump da barazanarsa ta tsoma baki domin goyon bayan masu zanga zangar kin jinin gwamnati.

Wani jami’in Amurka da bai so a fadi sunansa ba yace Amurka tana kwashe ma’aikata daga wasu muhimman sansanoninta a saboda karuwar tankiya.

Wani jami’in soja a kasar yammaci yace a bisa dukkan alamu Amurka ta yanke shawarar zata kai ma kasar Iran farmaki, amma kuma yace irin wannan dabi’a gwamnatin Trump ta saba nunawa na haddasa yanayin kokwanto a kan zata kai ne ko ba zata kai harin ba.

Amma kuma a fadarsa ta White House, shugaba Trump ya nuna alamun kamar yana jira ya ga yadda lamarin zai wakana ne, trump yace wata majiya mai tushe ta fada masa cewa yawan kashe kashe ya ragu, kuma babu wani shirin da aka yi a yanzu na zartas da hukumcin kisa a kan mutane masu yawa.

Wasu jami’an Turai guda biyu ma sun ce watakila nan da sa’o’i 24 Amurka zata kai hari a kan kasar Iran haka ma wani jami’in gwamnatin bani Isra’ila yace da ala mun shugaba Trump ya yanke shawarar zai tsoma hannu a Iran, amma ba a san irin farmakin da zai kai ko kuma lokacin kaiwa ba.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland
Next Post: Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
Kadan Daga Cikin Abubuwan Da Suka Faru A 2025 A Nan Amurka Amurka
Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.