Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
Published: December 12, 2025 at 10:54 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana shirin daukar sabbin ma’aikatan tsaro sama da 94,000 domin ƙarfafa yaki da tashin hankalin a faɗin ƙasar.

A cikin shirin ta, Hukumar Kula da Ayyukan ’Yan Sanda (PSC) tare da Rundunar ’Yan Sanda (NPF) za su dauki ’yan sanda 50,000, inda za’a bude shafin neman aikin daga ranar 15 ga watan Disamba 2025, zuwa 25 ga Janairu 2026.

A wata sanarwa daga Hukumar, an bayyana cewa daukar aikin ya biyo bayan umarnin Shugaba Bola Tinubu na ƙarfafa tsaron cikin gida da faɗaɗa ƙarfin ’yan sanda.

Ana bukatar masu neman aikin su mallaki takardar shaidar kammala karatun Sakandare ta SSCE/NECO ko makamantan su da ke da a ƙalla Credits biyar, ciki har da Turanci da Lissafi.

Wani jami’in soji wanda bashi da izinin magana na manema labarai yace، Rundunar Sojin kasa ta Najeriya na iya daukar sojoji 14,000. Majiyoyi kuma sun tabbatar da cewa Rundunar Sojin Ruwa da Ta Sama za su ƙara yawan ma’aikata.

A baya, Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta sanar da daukar ma’aikata 30,000 a hukumomin tsaron da ba na Soja ba (paramilitary).

Wannan na zuwa ne bayan Shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta baci kan tsaro a ranar 26 ga Nuwamba, 2025, tare da umarnin daukar ƙarin ma’aikata a hukumomin tsaron kasar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031
Next Post: Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa

Karin Labarai Masu Alaka

Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hawan Sallah Daga Masarautar Misau Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
  • Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.