Sojojin saman Nijeriya sun lalata sansanonin ƴan ta’adda a Arewa maso Gabas
Rundunar Sojin Sama ta Ƙasa (NAF) ta ƙara kaimi wajen kai hare-hare ta sama kan ‘yan tada kayar baya a yankin Arewa maso Gabas, inda ta aiwatar da jerin hare-hare masu ƙarfi kan sansanonin ‘yan ta’adda a Sambisa da yankunan Tumbuns.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Hulda da Jama’a da Watsa Labarai na rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar a ranar Juma’a, ya bayyana cewa an gudanar da wadannan hare-hare ne karkashin bangaren sama na Operation HADIN KAI.
Ya ce “bisa sahihan bayanan sirri, jiragen NAF sun kai hare-hare kai tsaye kan maboyar ‘yan ta’adda, inda suka lalata wuraren buya, suka kassara cibiyoyin kayayyaki, tare da halaka dimbin mayaka a hare-hare masu tsari da juna.”
Ejodame ya kara da cewa a ranar 30 ga watan Afrilu, “jiragen rundunar sun kai wani gagarumin harin sama a Alafa da ke yankin Sambisa, inda aka kai hari kan muhimman kayayyaki da cibiyoyin samar da kayan aiki na ‘yan ta’adda, aka kuma lalata su baki daya.”
Sanarwar ta kuma jiyo Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, yana cewa hare-haren za su ci gaba har sai an kawar da duk wata barazana.


