Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta bayyana cewa rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta, wanda ke ikirarin cewa an kona gidan Malam Nafiu Bala a Jihar Gombe, ba shi da tushe balle makama.
Sanarwar DSP Buhari Abdullahi, ANIPR, ANISMA Jami’in Hulda da Jama’a na ‘Yan Sanda Madadin Kwamishinan ‘Yan Sanda Rundunar ta jaddada cewa babu wani irin lamari da ya faru ko aka rubuta a ko’ina cikin jihar, don haka ta bayyana rahoton a matsayin labarin ƙarya da yaudara.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, mnips, fwc, psc(+), ya bukaci jama’a da su yi watsi da wannan jita-jita tare da ci gaba da gudanar da harkokinsu cikin kwanciyar hankali. Ya kuma tabbatar da cewa rundunar na ci gaba da daukar matakan tabbatar da tsaro da zaman lafiya a dukkan sassan jihar.


