Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe
Published: February 1, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da munanan hare-haren ’yan bindiga a Gombe, ta nemi a ɗauki matakin soji cikin gaggawa.

Majalisar Wakilai ta amince da wani kudiri na gaggawa da ya shafi bukatun jama’a dangane da yawaitar hare-haren ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Akko ta jihar Gombe, waɗanda suka yi sanadin mutuwar akalla mutane shida, sace wasu 20, tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin naira.

Kudirin, wanda Usman Bello Kumo ya gabatar, ya jawo hankalin ’yan majalisar kan sabbin hare-hare da aka kai cikin tsari a Garin Galadima, Pindiga, Garin Jaji, Laro da sauran al’ummomin da ke kewaye, lamarin da ya haddasa fargaba mai tsanani, kauracewar mazauna yankunan daga gidajensu, da kuma asarar hanyoyin samun abin dogaro.

Yayin gabatar da kudirin a zaman majalisa a Abuja, Kumo ya bayyana cewa hare-haren sun tilasta wa mazauna yankunan da dama gudun hijira, lamarin da ya ƙara tsananta matsalolin jin ƙai da kuma tabarbarewar tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Bayan amincewa da kudirin, Majalisar ta yanke shawarar kira ga Hukumar Kula da bayar da agajin gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da Hukumar Raya Arewa maso Gabas (NEDC) da su gaggauta samar da kayan agaji ga waɗanda abin ya shafa da kuma mutanen da suka rasa muhallan su a al’ummomin da abin ya shafa.

Haka kuma, ’yan majalisar sun yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya gaggauta umartar Babban Hafsan Tsaro da ya ƙaddamar da haɗaɗɗiyar rundunar tsaro domin korar ’yan bindigar da rushe sansanoninsu, tare da hana faruwar irin waɗannan hare-hare nan gaba.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya.
Next Post: Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga

Karin Labarai Masu Alaka

Tsofin Shugabanin Kasa Sun Karbi Bakoncin Hafsan Sojin Najeriya Tsaro
Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano Labarai
Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba Amurka
  • Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.