Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe
Published: February 1, 2026 at 5:10 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Wakilai ta yi Allah-wadai da munanan hare-haren ’yan bindiga a Gombe, ta nemi a ɗauki matakin soji cikin gaggawa.

Majalisar Wakilai ta amince da wani kudiri na gaggawa da ya shafi bukatun jama’a dangane da yawaitar hare-haren ’yan bindiga a ƙaramar hukumar Akko ta jihar Gombe, waɗanda suka yi sanadin mutuwar akalla mutane shida, sace wasu 20, tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin naira.

Kudirin, wanda Usman Bello Kumo ya gabatar, ya jawo hankalin ’yan majalisar kan sabbin hare-hare da aka kai cikin tsari a Garin Galadima, Pindiga, Garin Jaji, Laro da sauran al’ummomin da ke kewaye, lamarin da ya haddasa fargaba mai tsanani, kauracewar mazauna yankunan daga gidajensu, da kuma asarar hanyoyin samun abin dogaro.

Yayin gabatar da kudirin a zaman majalisa a Abuja, Kumo ya bayyana cewa hare-haren sun tilasta wa mazauna yankunan da dama gudun hijira, lamarin da ya ƙara tsananta matsalolin jin ƙai da kuma tabarbarewar tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Bayan amincewa da kudirin, Majalisar ta yanke shawarar kira ga Hukumar Kula da bayar da agajin gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da Hukumar Raya Arewa maso Gabas (NEDC) da su gaggauta samar da kayan agaji ga waɗanda abin ya shafa da kuma mutanen da suka rasa muhallan su a al’ummomin da abin ya shafa.

Haka kuma, ’yan majalisar sun yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya gaggauta umartar Babban Hafsan Tsaro da ya ƙaddamar da haɗaɗɗiyar rundunar tsaro domin korar ’yan bindigar da rushe sansanoninsu, tare da hana faruwar irin waɗannan hare-hare nan gaba.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya.
Next Post: Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga

Karin Labarai Masu Alaka

Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado Amurka
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
  • Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.