Gwamnatin jihar Filato ta gurfanar da mutane biyar a gaban kotu da take zargi da kai hari da kisan mutane fiye da talatin a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.
A ranar Jumma’ar da ta gabata ne gwamnatin jihar Filato ta shigar da karar wassu mutane biyar a gaban kotu, wanda jami’an tsaro na farin kaya ta DSS suka kama, bisa zargin kashe mutane fiye da talatin a karshen watan Maris na wannan shekara, a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.
Gwamnatin ta shigar da karar mutane hudu daga cikinsu kan laifin ta’addanci, yayinda mutum guda ake tuhumarsa da laifin hadin baki, kisa, mallakar makamai da safarar makamai da albarusai ba bisa ka’ida ba.
Da yake gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu, babban lauyan jihar, Philemon Audu Daffi yace laifin da mutanen suka aikata ya saba wa sashe na 269 da sashe na 270 na dokar Penal code na jihar Filato.
Rahoton da kakakin rundunar dake aikin wazadda zaman lafiya a jihar Filato ta Operation Enduring Peace, Chinonso Oteh ya aike wa manema labarai, bai bayyana ranar da za’a ci gaba da sauraron karar ba.
A halin da ake ciki dai, yayinda zaman lafiya ya dawo cikin birnin Jos, wassu da suka tsira da lafiyarsu, a lokacin tashin hankalin, sun bayyana cewa mabiya addinan da ba nasu ba sune suka boye su, don kar a hallaka su.
Malama Martha Kura tace ta gamu da fusatattun matasa ne yayinda ta fito kasuwa, amma al’ummar musulmi dake wurin suka kareta.
Shima Alhaji Nasiru Muhammad Ali wanda rikicin ya rutsa da shi a unguwar Eto-Baba, dake kusa da Anguwar Rukuba yace kirista ne suka boye shi.
Al’ummar jihar Filato dake son zaman lafiya dai suna kan fadakar da jama’a muhimmancin kyakkyawar hulda da zamantakewa don samun ci gaba.
Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos


