Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika

Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu
Published: April 22, 2026 at 5:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Filato ta gurfanar da mutane biyar a gaban kotu da take zargi da kai hari da kisan mutane fiye da talatin a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.

A ranar Jumma’ar da ta gabata ne gwamnatin jihar Filato ta shigar da karar wassu mutane biyar a gaban kotu, wanda jami’an tsaro na farin kaya ta DSS suka kama, bisa zargin kashe mutane fiye da talatin a karshen watan Maris na wannan shekara, a Anguwar Rukuba dake karamar hukumar Jos ta Arewa.

Gwamnatin ta shigar da karar mutane hudu daga cikinsu kan laifin ta’addanci, yayinda mutum guda ake tuhumarsa da laifin hadin baki, kisa, mallakar makamai da safarar makamai da albarusai ba bisa ka’ida ba.

Da yake gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu, babban lauyan jihar, Philemon Audu Daffi yace laifin da mutanen suka aikata ya saba wa sashe na 269 da sashe na 270 na dokar Penal code na jihar Filato.

Rahoton da kakakin rundunar dake aikin wazadda zaman lafiya a jihar Filato ta Operation Enduring Peace, Chinonso Oteh ya aike wa manema labarai, bai bayyana ranar da za’a ci gaba da sauraron karar ba.

A halin da ake ciki dai, yayinda zaman lafiya ya dawo cikin birnin Jos, wassu da suka tsira da lafiyarsu, a lokacin tashin hankalin, sun bayyana cewa mabiya addinan da ba nasu ba sune suka boye su, don kar a hallaka su.

Malama Martha Kura tace ta gamu da fusatattun matasa ne yayinda ta fito kasuwa, amma al’ummar musulmi dake wurin suka kareta.

Shima Alhaji Nasiru Muhammad Ali wanda rikicin ya rutsa da shi a unguwar Eto-Baba, dake kusa da Anguwar Rukuba yace kirista ne suka boye shi.

Al’ummar jihar Filato dake son zaman lafiya dai suna kan fadakar da jama’a muhimmancin kyakkyawar hulda da zamantakewa don samun ci gaba.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260422-WA0056.mp3
Afrika, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci
Next Post: Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa

Karin Labarai Masu Alaka

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Afrika Ta Kudu Ta Dora Haraji Mai Yawa Kan Karafa Afrika
  • Ga Fili Ga Doki Najeriya
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
  • Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
  • Amurka Zata Kara Tura Sojoji Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.