Rahotanni daga jihar Zamfara na tabbatar da cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun sace shugaban karamar hukumar Bungudu, Nura Umar Abdullahi, bayan sun kai hari gidansa cikin dare.
Majiyoyi sun ce maharan sun yi galaba kan jami’an tsaron da ke gadin gidan kafin su yi awon gaba da shugaban karamar hukumar tare da wasu daga cikin iyalansa.
Rahotanni sun kuma ce jami’an tsaro da dakarun Operation FANSAN YAMMA sun kai dauki, inda suka ceto mutum biyar daga cikin iyalan shugaban karamar hukumar, yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike da kokarin ceto shi.
Harin ya yi sanadin mutuwar wasu jami’an tsaro da suka yi yunkurin dakile maharan, yayin da hukumomin tsaro suka ce sun fara gudanar da hadin gwiwar neman ceto shugaban karamar hukumar da kuma kamo wadanda suka aikata harin.


