Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed Kauran Daular Usmaniyya, ya bayyana alhininsa kan rasuwar Malam Abdullahi Sule, wanda aka fi sani da “Madaki”, ma’aikacin ɗaukar hoto na ENG da ke aiki da tawagar manema labarai ta Gidan Gwamnatin jihar Bauchi.
Malam Abdullahi Sule ya rasu ne a safiyar Alhamis, 10 ga Satumba, 2026, bayan fama da gajeriyar rashin lafiya.
A cikin wata sanarwa, Gwamna Bala Mohammed ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, ‘yan tawagar manema labarai ta Gidan Gwamnatin Jihar Bauchi, ƙungiyar ’yan jaridu ta Najeriya, NUJ, abokai da abokan aikinsa, tare da al’ummar Jihar Bauchi baki ɗaya.
Gwamnan ya bayyana marigayin a matsayin ƙwararren ma’aikacin kafafen yaɗa labarai, mai ƙwazo, jajircewa, sauƙin kai da son zaman lafiya, wanda kyawawan halayensa suka sanya mutane da dama suka ƙaunace shi.
Ya ce Malam Abdullahi Sule ya kasance ma’aikaci mai biyayya da kishin aiki, wanda ya gudanar da ayyukansa cikin ƙwarewa da sadaukarwa, musamman wajen ɗaukar hotuna da adana tare da yaɗa ayyukan gwamnatin Jihar Bauchi.
Gwamna Bala Mohammed ya ce rasuwar “Madaki” babban rashi ne ba ga iyalansa da abokan aikinsa kaɗai ba, har ma ga al’ummar kafafen yaɗa labarai da Jihar Bauchi baki ɗaya.
Ya bayyana shi a matsayin mutum mai sauƙin kai, nagarta da kyakkyawar mu’amala da jama’a, tare da nuna halin zaman lafiya a tsawon rayuwarsa.
Gwamnan ya roƙi Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya jiƙansa, Ya sa Aljannatul Firdaus ce makomarsa, sannan Ya bai wa iyalansa, abokan aikinsa, abokansa da sauran waɗanda rasuwar ta shafa ƙarfin zuciya da haƙurin jure wannan babban rashi.
Haka kuma, Gwamna Bala Mohammed ya yi kira ga al’ummar kafafen yaɗa labarai da sauran masu zaman makoki da su yi haƙuri tare da tuna cewa mutuwa hanya ce da babu makawa kowane ɗan Adam zai bi.
Kuma tuni an gudanar da sallar jana’izar marigayi Malam Abdullahi Sule “Madaki” a ranar Alhamis, 10 ga Satumba, 2026, da ƙarfe 9:00 na safe, a Filin Barewa, daura da Maman Kapaya, Unguwan Kur, Railway, Bauchi.


