Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika
  • Yara Miliyan 16 Sun Amfana Da Azithromycin A Karkashin Shirin SARMAAN Afrika

Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
Published: September 10, 2026 at 10:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed Kauran Daular Usmaniyya, ya bayyana alhininsa kan rasuwar Malam Abdullahi Sule, wanda aka fi sani da “Madaki”, ma’aikacin ɗaukar hoto na ENG da ke aiki da tawagar manema labarai ta Gidan Gwamnatin jihar Bauchi.

Malam Abdullahi Sule ya rasu ne a safiyar Alhamis, 10 ga Satumba, 2026, bayan fama da gajeriyar rashin lafiya.

A cikin wata sanarwa, Gwamna Bala Mohammed ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, ‘yan tawagar manema labarai ta Gidan Gwamnatin Jihar Bauchi, ƙungiyar ’yan jaridu ta Najeriya, NUJ, abokai da abokan aikinsa, tare da al’ummar Jihar Bauchi baki ɗaya.

Gwamnan ya bayyana marigayin a matsayin ƙwararren ma’aikacin kafafen yaɗa labarai, mai ƙwazo, jajircewa, sauƙin kai da son zaman lafiya, wanda kyawawan halayensa suka sanya mutane da dama suka ƙaunace shi.

Ya ce Malam Abdullahi Sule ya kasance ma’aikaci mai biyayya da kishin aiki, wanda ya gudanar da ayyukansa cikin ƙwarewa da sadaukarwa, musamman wajen ɗaukar hotuna da adana tare da yaɗa ayyukan gwamnatin Jihar Bauchi.

Gwamna Bala Mohammed ya ce rasuwar “Madaki” babban rashi ne ba ga iyalansa da abokan aikinsa kaɗai ba, har ma ga al’ummar kafafen yaɗa labarai da Jihar Bauchi baki ɗaya.

Ya bayyana shi a matsayin mutum mai sauƙin kai, nagarta da kyakkyawar mu’amala da jama’a, tare da nuna halin zaman lafiya a tsawon rayuwarsa.

Gwamnan ya roƙi Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa, Ya jiƙansa, Ya sa Aljannatul Firdaus ce makomarsa, sannan Ya bai wa iyalansa, abokan aikinsa, abokansa da sauran waɗanda rasuwar ta shafa ƙarfin zuciya da haƙurin jure wannan babban rashi.

Haka kuma, Gwamna Bala Mohammed ya yi kira ga al’ummar kafafen yaɗa labarai da sauran masu zaman makoki da su yi haƙuri tare da tuna cewa mutuwa hanya ce da babu makawa kowane ɗan Adam zai bi.

Kuma tuni an gudanar da sallar jana’izar marigayi Malam Abdullahi Sule “Madaki” a ranar Alhamis, 10 ga Satumba, 2026, da ƙarfe 9:00 na safe, a Filin Barewa, daura da Maman Kapaya, Unguwan Kur, Railway, Bauchi.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko
Next Post: CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
Zaben Osun 2026: Darasi Ga APC, Gargadi Ga ADC, Nasara Ga Adeleke Afrika
Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
  • Amy Hunt Ta Zama Sabuwar Tauraruwar Wasannin Guje-guje Ta Birtaniya Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
  • Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.