Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe
Published: December 17, 2025 at 2:18 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe a Najeriya ta sanar da cewa mutum 11 sun kamu da zazzabin Lassa, inda mutum ɗaya ya rasu.

Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya a Jihar Gombe, Dokta Habu, ne ya bayyana hakan yayin wani taron saka ido da mayar da martani kan barkewar cututtuka da aka gudanar a Gombe.

Dokta Habu ya ce marigayin ya fara nuna alamun zazzabin Lassa ne yayin da yake jihar Taraba, kafin daga bisani a turo shi Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Gombe, domin jinya.

Ya kara da cewa, ta fuskar kididdigar lafiyar jama’a, lamarin ana daukarsa a matsayin na jihar Taraba.

“An kula da marasa lafiyar a Gombe, amma asalin zazzabin daga Taraba ya fito, an mayar da lambar EPID zuwa jihar Taraba,” in ji shi.

Ya bayyana cewa yawancin mutanen da aka tabbatar sun kamu da zazzabin Lassa na daga cikin mutanen da ke zuwa jihar Taraba domin aikin noma.

Kwamishinan ya jaddada cewa ko da mutum guda ne aka tabbatar ya kamu da cutar, ana daukar sa a matsayin barkewar cuta, saboda tsananin hadarinta.

Dokta Habu ya ce Gombe ta samu nasarar dakile barkewar cututtuka da dama sakamakon shiri tun kafin lokaci, tare da saurin daukar mataki da hadin gwiwa da hukumomi kamar Hukumar Kula da Cututtuka ta Kasa (NCDC), Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da UNICEF.

Ya ce an kira taron yankin ne domin karfafa tsarin sa ido da daukar mataki kan barkewar cututtuka a jihohin yankin, biyo bayan yawaitar barkewar cututtuka a jihohin Adamawa, Taraba, Bauchi da Plateau.

A karshe, kwamishinan ya bukaci a rika gano cututtuka da wuri, bayar da rahoto cikin gaggawa, da karfafa hadin kai tsakanin jihohi, domin dakile yaduwar zazzabin Lassa da sauran cututtuka masu yaduwa a cikin al’umma

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Next Post: Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe Najeriya
Kotun Tarayya Tabada Belin Nasiru El Rufai Afrika
Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Afrika Ta Kudu Ta Dora Haraji Mai Yawa Kan Karafa Afrika
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
  • An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.