Ranar Litinin Lauyoyin gwamnati a kenya suka gurfanar da wani dan kasar gaban kotu kan zargin samarda kiyashi da nau’in su ga masu fasa korin irin wadan nan halittu, a kokarin da gwamnati take yi na hana fasa-korin wadan nan halittu daga kasar.
A wani bayani da ta wallafa a dandalin X, ofishin Daraktan lauyoyin gwamnatin kasar tace ta gurfanar da wani dan kasar Charles Mwangi a gaban kotu dake babbar tashar jirgin saman kasar da ake kira Jomo Kenyata International Airport.
Sakamakon binciken gidansa da ‘Yan sanda suka yi sun gano irin nau’in kiyashi da suka fi zama a lambu dubu daya, da kuma wasu 113 wadanda tuni aka saka su cikin robobin allura, da kuma robobin yin allurar 503 wadanda babu komi a ciki.


