Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana
Published: January 8, 2026 at 1:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dama dai tun a watan Junairun shekarar da ta gabata ne tsohon ministan kuɗaɗen Ghana, Ken Ofori-Atta ya tsere daga Accra zuwa Amurka da sunan neman lafiya.

Tsohon ministan wanda gwamnatin Accra ta zarge shi da badaƙalar maƙudan kuɗaɗe, har ma ta ce ya tsere daga ƙasar ne saboda gudun fuskantar shari’a, ya nemi tsawaita zamansa a Washington a cewar lauyoyinsa.

To amma jami’an hukumar shige da fice na ƙasar sun kama shi, inda zuwa yanzu babu masaniya game da inda aka ajiye shi a cikin Amurkan.

Sanarwar da tawagar lauyoyinsa suka fitar, ta ce suna tatttaunawa da jami’an tsaron Washington don ganin an sake shi nan bada jimawa ba, a cewarsu shi ma tsohon ministan yana bai wa jami’an haɗin kai.

Ofori-Atta, dai ya kasance ministan kuɗi na Ghana tun daga shekarar 2017 har zuwa ta 2024, zamanin mulkin tsohon shugaban ƙasar Nana Akufo-Addo, inda ya jagoranci aiwatar da sauye-sauye da dama a fannin tattalin arziƙin ƙasar, wanda gwamnatin John Dramani Mahama ke adawa da su.

Afrika, Amurka

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara
Next Post: An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba.

Karin Labarai Masu Alaka

Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
Iran Da Amurka Sun Gindayawa Juna Ka’idojin Tsagaita Wuta Afrika
An Kaddamar Da Jigilar Maniyyata Aikin Hajji A Abuja Afrika
Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Ta Kubutar Da ‘Yan Kasar Da Suke Taya Sojojin Rasha Yaki Afrika
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Gwamnatin Kano Zata Dauki Mataki Game Da Kisan Dorayi Tsaro
  • Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
  • Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito Afrika
  • Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.