Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana
Published: January 8, 2026 at 1:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dama dai tun a watan Junairun shekarar da ta gabata ne tsohon ministan kuɗaɗen Ghana, Ken Ofori-Atta ya tsere daga Accra zuwa Amurka da sunan neman lafiya.

Tsohon ministan wanda gwamnatin Accra ta zarge shi da badaƙalar maƙudan kuɗaɗe, har ma ta ce ya tsere daga ƙasar ne saboda gudun fuskantar shari’a, ya nemi tsawaita zamansa a Washington a cewar lauyoyinsa.

To amma jami’an hukumar shige da fice na ƙasar sun kama shi, inda zuwa yanzu babu masaniya game da inda aka ajiye shi a cikin Amurkan.

Sanarwar da tawagar lauyoyinsa suka fitar, ta ce suna tatttaunawa da jami’an tsaron Washington don ganin an sake shi nan bada jimawa ba, a cewarsu shi ma tsohon ministan yana bai wa jami’an haɗin kai.

Ofori-Atta, dai ya kasance ministan kuɗi na Ghana tun daga shekarar 2017 har zuwa ta 2024, zamanin mulkin tsohon shugaban ƙasar Nana Akufo-Addo, inda ya jagoranci aiwatar da sauye-sauye da dama a fannin tattalin arziƙin ƙasar, wanda gwamnatin John Dramani Mahama ke adawa da su.

Afrika, Amurka

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara
Next Post: An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba.

Karin Labarai Masu Alaka

APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Afrika
Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.