Wata biyu a jere, Najeriya bata bada lasisin shigo da man fetur daga ketare ba, yayinda hukumomin kasar suka fara aiki da dokar kasar data ce Najeriya zata bada izinin a shigo da mai daga ketare ne kawai idan ta fuskanci karanci a cikin gida.
Alkaluma daga hukumomin kula da harkokin mai na kasar sun nuna cewa ba’a bada lasisin shigo da mai cikin watan Febwairu ba, haka nan Kungiyar masu masana’antun tace mai suna cewa zuwa yanzu dai cikin watan Maris ba su ga an bada lasisin shigo da mai daga ketare ba. Idan hakan ya dore ya nuna nasara da kamfanin tace mai na Dangote ya samu, wadda a bara ya shigar da kara a gaban kotu na neman hana shigo da mai daga ketare.
A wani al’amari na daban, ranar Litinin ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ta gargadi ‘yan kasarta da suke Najeriya cewa akwai “barazanar harin ta’addanci,” kan muradun Amurka a kasar da suka hada da makarantu, kamar yadda sanarwar da ta bayar a ranar Litinin.
Ofishin jakadancin yana cikin Shirin ko ta kwana, tun lokacin da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare hare kan Iran. Ofishin jakadancin ya bukaci Amurkawa da suyi taka-tsan tsan idan za su ziyarci ofishin jakadancin dake Abuja da kuma Legas, da kuma makarantu masu alaka da ita.


