Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: December 9, 2025 at 7:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 9, 2025

Burkina Faso ta tsare sojojin Najeriya 11, ta kuma kwace jirgin saman NAF saboda shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin sojin Burkina Fason ce, ta tabbatar da tsare jami’an sojan Najeriya 11 tare da kwace wani jirgin dakon kaya na rundunar sojin saman Najeriya (NAF) bayan ya shiga sararin samaniyar kasar ba tare da izini ba sannan ya yi saukar gaggawa.

A cikin sanarwar da Kungiyar Kasashen Sahel (Alliance of Sahel States – AES) ta fitar a daren Litinin, an ce jirgin C-130 na sojin saman Najeriya ya yi saukar gaggawa a Bobo Dioulasso a ranar 8 ga Disamba, 2025, sakamakon matsalar fasaha yayin da yake shawagi a cikin sararin samaniyar Burkina Faso ba tare da izinin shiga ba.

AES dai ƙungiya ce da ta ƙunshi Burkina Faso, Nijar da Mali, dukkaninsu kuma suna ƙarƙashin mulkin soja.

Hukumomin kasar sun bayyana cewa jirgin na ɗauke da matuka biyu da kuma fasinjoji tara  dukkansu jami’an sojan Najeriya ne, ana tsare da su a halin yanzu a hannun hukumomin Burkina Faso.

Kungiyar AES ta yi Allah wadai da lamarin, tana mai cewa hakan babban take hakkin kasa da tauye ikon mallakar sararin samaniya ne amma kuma an kaddamar da cikakken bincike domin gano hakikanin dalilin shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

A martaninsu, AES ta sanar da cewa dakarun kasashen uku sun shiga matakin tsaro mafi girma ne, haka kuma, an bai wa rundunonin tsaro izinin amfani da makaman kare sararin samaniya da na harbo jiragen da zasu karya dokokin sararin samaniyar su.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato
Next Post: Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025:

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
Gombe Ta Yi Fice A Duniya: Maryam Dan’azumi Ta Lashe Gasar Alƙur’ani Na Ƙasa Da Ƙasa Afrika
Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
  • Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.