Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba
Published: December 9, 2025 at 7:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 9, 2025

Burkina Faso ta tsare sojojin Najeriya 11, ta kuma kwace jirgin saman NAF saboda shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin sojin Burkina Fason ce, ta tabbatar da tsare jami’an sojan Najeriya 11 tare da kwace wani jirgin dakon kaya na rundunar sojin saman Najeriya (NAF) bayan ya shiga sararin samaniyar kasar ba tare da izini ba sannan ya yi saukar gaggawa.

A cikin sanarwar da Kungiyar Kasashen Sahel (Alliance of Sahel States – AES) ta fitar a daren Litinin, an ce jirgin C-130 na sojin saman Najeriya ya yi saukar gaggawa a Bobo Dioulasso a ranar 8 ga Disamba, 2025, sakamakon matsalar fasaha yayin da yake shawagi a cikin sararin samaniyar Burkina Faso ba tare da izinin shiga ba.

AES dai ƙungiya ce da ta ƙunshi Burkina Faso, Nijar da Mali, dukkaninsu kuma suna ƙarƙashin mulkin soja.

Hukumomin kasar sun bayyana cewa jirgin na ɗauke da matuka biyu da kuma fasinjoji tara  dukkansu jami’an sojan Najeriya ne, ana tsare da su a halin yanzu a hannun hukumomin Burkina Faso.

Kungiyar AES ta yi Allah wadai da lamarin, tana mai cewa hakan babban take hakkin kasa da tauye ikon mallakar sararin samaniya ne amma kuma an kaddamar da cikakken bincike domin gano hakikanin dalilin shiga kasar ba bisa ka’ida ba.

A martaninsu, AES ta sanar da cewa dakarun kasashen uku sun shiga matakin tsaro mafi girma ne, haka kuma, an bai wa rundunonin tsaro izinin amfani da makaman kare sararin samaniya da na harbo jiragen da zasu karya dokokin sararin samaniyar su.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato
Next Post: Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025:

Karin Labarai Masu Alaka

Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika
Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
  • Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.