Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki
Published: February 26, 2026 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Afrika ta kudu da Kenya a ranar Alhamis suke kara bayyana cewa ‘yan kasashen masu yawa ne aka yaudare su shiga yakin Rasha da Ukraine, domin hukumomi a Pretoria sun bada rahoton ‘yan kasar biyu sun mutu a fagen daga, yayinda wata kotu a Nairobi ta tuhumi wani mutum da laifin safarar ‘yan kasar 25 domin suyi yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Afrika ta kudu ta fada cewa ‘yan kasar biyu da suka mutu a fagen yaki basa cikin ‘yan kasar su 17 da aka yaudara suka taya Rasha yaki a Ukraine, wadanda galibin su an ceto su sun koma kasar, kamar yadda wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Alhamis. Ma’aikatar bata fadi lokaci da kuma yanayin da ya kai ga mutuwar mutanen biyu ba.

Hukumomin Rasha sun musanta cewa suna daukar ‘yan kasashen Afirka aikin soja ba bisa ka’ida ba domin yakinta da Ukraine.

“gwamnati tana ci gaba da binciken kungiyoyi da suke da hanu wajen daukar ‘yan kasa zuwa Rasha, da zummar hukunta dukkan wadanda suke da hanu ciki,” kamar yadda doka ta tanada, ma’aikatar harkokin wajen Afirka ta kudun ta fada.

A Nairobi, kotu ta tuhumi wani dan kasar mai suna Festus Arasa Omwamba, darektan wani kamfanin samarwa mutane ayyyukan yi da laifin safarar mutane zuwa Rasha ta hanyoyin yaudara, kamar yadda ofishin Daraktan gabatar da kararraki na kasar ya fada.

Ma’aikatar shari’ar tace an ceto mutane 22 cikin 25, a wani daki a karamar hukumar Machakos da bashi da nisa da babban birnin kasar cikin watan Nuwamban bara. Uku daga cikin wannan adadi tuni suka sapmi kansu a fagen daga a Ukraine.

Fiye da ‘yan kasashen Afirka dubu daya da dari bakwai ne suke yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi
Next Post: Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar Amurka
Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
  • Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
  • An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe Labarai
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.