Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki
Published: February 26, 2026 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Afrika ta kudu da Kenya a ranar Alhamis suke kara bayyana cewa ‘yan kasashen masu yawa ne aka yaudare su shiga yakin Rasha da Ukraine, domin hukumomi a Pretoria sun bada rahoton ‘yan kasar biyu sun mutu a fagen daga, yayinda wata kotu a Nairobi ta tuhumi wani mutum da laifin safarar ‘yan kasar 25 domin suyi yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Afrika ta kudu ta fada cewa ‘yan kasar biyu da suka mutu a fagen yaki basa cikin ‘yan kasar su 17 da aka yaudara suka taya Rasha yaki a Ukraine, wadanda galibin su an ceto su sun koma kasar, kamar yadda wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ranar Alhamis. Ma’aikatar bata fadi lokaci da kuma yanayin da ya kai ga mutuwar mutanen biyu ba.

Hukumomin Rasha sun musanta cewa suna daukar ‘yan kasashen Afirka aikin soja ba bisa ka’ida ba domin yakinta da Ukraine.

“gwamnati tana ci gaba da binciken kungiyoyi da suke da hanu wajen daukar ‘yan kasa zuwa Rasha, da zummar hukunta dukkan wadanda suke da hanu ciki,” kamar yadda doka ta tanada, ma’aikatar harkokin wajen Afirka ta kudun ta fada.

A Nairobi, kotu ta tuhumi wani dan kasar mai suna Festus Arasa Omwamba, darektan wani kamfanin samarwa mutane ayyyukan yi da laifin safarar mutane zuwa Rasha ta hanyoyin yaudara, kamar yadda ofishin Daraktan gabatar da kararraki na kasar ya fada.

Ma’aikatar shari’ar tace an ceto mutane 22 cikin 25, a wani daki a karamar hukumar Machakos da bashi da nisa da babban birnin kasar cikin watan Nuwamban bara. Uku daga cikin wannan adadi tuni suka sapmi kansu a fagen daga a Ukraine.

Fiye da ‘yan kasashen Afirka dubu daya da dari bakwai ne suke yaki a bangaren Rasha a fafatawar da kasar take yi da Ukraine.

Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi
Next Post: Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa Labarai
Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Za’a Saka Tarihin Trump A Manhajar Makarantu Don Jajircewasa Da Kwazo Amurka
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.