Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere
Published: April 20, 2026 at 2:01 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Al’ummar yankin Mushere dake karamar hukumar Bokkos a jihar Filato sun bukaci gwamnatin jihar da tabi matakan da dokar kasa da ta ayyana, waje dawo musu da babban hakiminsu da ta Sauke daga sarauta.

Kimanin makonni biyu da suka gabata ne gwamnatin jihar Filato ta tumbuke babban hakimin yankin Mushere a karamar hukumar Bakkos a jihar Filato, Dakta Julius Dibilang, lamarin da ya janyo zanga-zanga da matan yankin suka yi tsirara.

Shugaban kungiyar raya al’ummar Mushere, Duwaf Bosco yace al’ummar yankin basu fahimci hujjar da gwamnati ta bayar na cire sarkin nasu ba.

Yankin na Mushere, inda tsohon gwamnan jihar Filato, Sanata Joshua Dariye ya fito, yayi shekaru bakwai babu hakimi, tun bayan rasuwar tsohon hakimin a shekarar dubu biyu da goma sha takwas, kafin a watan satumban bara, gwamnatin jihar ta nada Dakta Julius Dibilang a matsayin babban hakimin yankin.

Daya daga cikin matan da suka yi zanga-zanga kan cire sarkin tace yanzu sun kasance ba jagora, don haka zasu fuskanci matsaloli da dama.

To sai dai a bangaren gwamnati, gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang ya bayyana cewa sun sami hakimin da laifin da kotu ta yanke masa hukunci da bai bayyana ba har sai bayan da aka bashi takarda.

Gwamnan ya kara da cewa, bayan sun sami shaidu masu gamsarwa daga wadanda suka yi korafin nada sarkin, ya zamo dole gwamnati ta janye takardar amincewa da sarautar, saboda doka ta haramta wa duk wanda kotu ta same shi da laifi rike ko wani irin mukami, har sai kotun ta warware hukuncin.

A halin da ake ciki dai, cire hakimin na Mushere ya janyo rarrabuwar kawunan al’ummar yankin, wanda wassu bayanai ke nuni da cewa bisa al’ada, ba zai yiwu a sake zaben wani sarki ba, har sai wannan sarkin ya bar duniya, yayinda wassu ke cewa za’a iya zaben wani hakimin ya maye gurbinsa.

Wakiliyar GTA Hausa Amurka Ke Magana Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/AUD-20260420-WA0101.mp3
Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
Next Post: An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
Iran: Za A Gudanar Da Jana’izar Khamenei Bayan Kwanaki Goma Na Muharram Afrika
Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa Afrika
Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dr. Kabiru Hassan Ya Kammala Wa’adinsa A GOGIS, Ya Yi Bitar Sauye-Sauyen Harkokin Filaye Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Da Iran Suna Cigaba Da Tattaunawa Amurka
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
  • NEDC Ta Fara Shirin Kera Sanitary Pads A Gombe Domin Samar Da Sana’o’i Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.