Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
Published: April 22, 2026 at 8:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Aikin Hajjin 2026: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya

​Hukumar Jin Daɗin Alhazzai ta Najeriya (NAHCON) ta kammala shirin tura tawagar jami’anta na musamman zuwa ƙasa mai tsarki a ranar 27 ga watan Afrilu, domin yin kwasan-kwasai da kuma samar da dukkan abubuwan da suka kamata kafin fara jigilar maniyyata.

​Wannan mataki na zuwa ne kwanaki kaɗan kafin ranar 3 ga watan Mayu, wadda ita ce ranar da aka tsara za a fara jigilar rukunin farko na maniyyatan Najeriya na shekarar 2026 zuwa Saudiyya.

Tawagar, wadda aka fi sani da ‘Advance Team’, ta ƙunshi jami’ai daga sassa daban-daban da suka haɗa da ​Ma’aikatan kula da masaukan alhazzai, ​Jami’an lafiya da masu kula da abinci, ​Tawagar kula da fasfo da kuma jigilar kaya.

​Babban aikin wannan tawaga shi ne tabbatar da cewa an kammala gyara masaukai, an tantance wuraren abinci, kuma an daidaita dukkan tsare-tsaren sufuri domin kauce wa duk wata matsala da za ta iya tasowa lokacin da alhazzai suka fara isa.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa tura jami’an da wuri wani ɓangare ne na sabon tsarin da aka fito da shi domin tabbatar da cewa aikin Hajjin bana ya gudana cikin nasara da natsuwa. Ana sa ran tawagar za ta haɗa gwiwa da hukumomin Saudiyya don tabbatar da cewa komai ya tafi daidai da tsarin da aka tsara.

​Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da maniyyata a faɗin ƙasar nan suke ci gaba da karɓar bita da kuma shirye-shiryen ƙarshe kafin fara kira na jigilar su zuwa ƙasa mai tsarki.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
Next Post: Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Shiga Takara Wa’adi Na Biyu Afrika
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.