Aikin Hajjin 2026: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
Hukumar Jin Daɗin Alhazzai ta Najeriya (NAHCON) ta kammala shirin tura tawagar jami’anta na musamman zuwa ƙasa mai tsarki a ranar 27 ga watan Afrilu, domin yin kwasan-kwasai da kuma samar da dukkan abubuwan da suka kamata kafin fara jigilar maniyyata.
Wannan mataki na zuwa ne kwanaki kaɗan kafin ranar 3 ga watan Mayu, wadda ita ce ranar da aka tsara za a fara jigilar rukunin farko na maniyyatan Najeriya na shekarar 2026 zuwa Saudiyya.
Tawagar, wadda aka fi sani da ‘Advance Team’, ta ƙunshi jami’ai daga sassa daban-daban da suka haɗa da Ma’aikatan kula da masaukan alhazzai, Jami’an lafiya da masu kula da abinci, Tawagar kula da fasfo da kuma jigilar kaya.
Babban aikin wannan tawaga shi ne tabbatar da cewa an kammala gyara masaukai, an tantance wuraren abinci, kuma an daidaita dukkan tsare-tsaren sufuri domin kauce wa duk wata matsala da za ta iya tasowa lokacin da alhazzai suka fara isa.
Hukumar NAHCON ta bayyana cewa tura jami’an da wuri wani ɓangare ne na sabon tsarin da aka fito da shi domin tabbatar da cewa aikin Hajjin bana ya gudana cikin nasara da natsuwa. Ana sa ran tawagar za ta haɗa gwiwa da hukumomin Saudiyya don tabbatar da cewa komai ya tafi daidai da tsarin da aka tsara.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da maniyyata a faɗin ƙasar nan suke ci gaba da karɓar bita da kuma shirye-shiryen ƙarshe kafin fara kira na jigilar su zuwa ƙasa mai tsarki.


