Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika

Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
Published: April 22, 2026 at 8:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Aikin Hajjin 2026: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya

​Hukumar Jin Daɗin Alhazzai ta Najeriya (NAHCON) ta kammala shirin tura tawagar jami’anta na musamman zuwa ƙasa mai tsarki a ranar 27 ga watan Afrilu, domin yin kwasan-kwasai da kuma samar da dukkan abubuwan da suka kamata kafin fara jigilar maniyyata.

​Wannan mataki na zuwa ne kwanaki kaɗan kafin ranar 3 ga watan Mayu, wadda ita ce ranar da aka tsara za a fara jigilar rukunin farko na maniyyatan Najeriya na shekarar 2026 zuwa Saudiyya.

Tawagar, wadda aka fi sani da ‘Advance Team’, ta ƙunshi jami’ai daga sassa daban-daban da suka haɗa da ​Ma’aikatan kula da masaukan alhazzai, ​Jami’an lafiya da masu kula da abinci, ​Tawagar kula da fasfo da kuma jigilar kaya.

​Babban aikin wannan tawaga shi ne tabbatar da cewa an kammala gyara masaukai, an tantance wuraren abinci, kuma an daidaita dukkan tsare-tsaren sufuri domin kauce wa duk wata matsala da za ta iya tasowa lokacin da alhazzai suka fara isa.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa tura jami’an da wuri wani ɓangare ne na sabon tsarin da aka fito da shi domin tabbatar da cewa aikin Hajjin bana ya gudana cikin nasara da natsuwa. Ana sa ran tawagar za ta haɗa gwiwa da hukumomin Saudiyya don tabbatar da cewa komai ya tafi daidai da tsarin da aka tsara.

​Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da maniyyata a faɗin ƙasar nan suke ci gaba da karɓar bita da kuma shirye-shiryen ƙarshe kafin fara kira na jigilar su zuwa ƙasa mai tsarki.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
Next Post: Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta

Karin Labarai Masu Alaka

An Ga Watan Ramadan A Najeriya Da Nijar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Shugaban Ƙasar Koriya Ta Arewa Ya Halarci Gwajin Makami Mai Linzamin Kasar Labarai
  • Rasha Ta Yiwa Amurka Tayin Daina Bada Bayanan Sirri Afrika
  • Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka Afrika
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.