Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
Published: April 22, 2026 at 8:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Aikin Hajjin 2026: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya

​Hukumar Jin Daɗin Alhazzai ta Najeriya (NAHCON) ta kammala shirin tura tawagar jami’anta na musamman zuwa ƙasa mai tsarki a ranar 27 ga watan Afrilu, domin yin kwasan-kwasai da kuma samar da dukkan abubuwan da suka kamata kafin fara jigilar maniyyata.

​Wannan mataki na zuwa ne kwanaki kaɗan kafin ranar 3 ga watan Mayu, wadda ita ce ranar da aka tsara za a fara jigilar rukunin farko na maniyyatan Najeriya na shekarar 2026 zuwa Saudiyya.

Tawagar, wadda aka fi sani da ‘Advance Team’, ta ƙunshi jami’ai daga sassa daban-daban da suka haɗa da ​Ma’aikatan kula da masaukan alhazzai, ​Jami’an lafiya da masu kula da abinci, ​Tawagar kula da fasfo da kuma jigilar kaya.

​Babban aikin wannan tawaga shi ne tabbatar da cewa an kammala gyara masaukai, an tantance wuraren abinci, kuma an daidaita dukkan tsare-tsaren sufuri domin kauce wa duk wata matsala da za ta iya tasowa lokacin da alhazzai suka fara isa.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa tura jami’an da wuri wani ɓangare ne na sabon tsarin da aka fito da shi domin tabbatar da cewa aikin Hajjin bana ya gudana cikin nasara da natsuwa. Ana sa ran tawagar za ta haɗa gwiwa da hukumomin Saudiyya don tabbatar da cewa komai ya tafi daidai da tsarin da aka tsara.

​Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da maniyyata a faɗin ƙasar nan suke ci gaba da karɓar bita da kuma shirye-shiryen ƙarshe kafin fara kira na jigilar su zuwa ƙasa mai tsarki.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
Next Post: Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai Labarai
Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • Margayi Shugaba Muhammadu Buhari 1942-2025 Labarai
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
  • Hawan Sallah Daga Masarautar Misau Afrika
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.