Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi
Published: January 27, 2026 at 8:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rawar da China take takawa a zaman wacce take kan gaba wajen bada bashi ga kasashe masu tasowa, ya sauya cikin shekaru 10 da suka wuce, yayin da sabbin basussuka ga kasashe matalauta yake faduwa, yawan kudade da kasashen suke biyan China sun karu sosai, kamar yadda alkaluma daga wata cibiya da ake kira ONE DATA suka nuna.

Chanjin yana zuwa ne a dai dai lokacin da basussuka da kasashe matalauta suke karba daga kungiyoyi da hukumomin kasa da kasa suka karu, da kamar kashi 124 cikin shekaru 10 da suka wuce, wanda yanzu sune ke bada kashi 56 cikin dari na basussuka da kasashen suke karpa daga ketare, da suka kai kimnin dala bilyan 379 da aka bayar tsakanin shekara ta 2020-2024, kididdigar ta nuna.

A bayanai da ake da su na baya bayan nan, daga shekara ta 2020-2024, Afirka taga tasirin mafi girma inda kudade dala bilyan 30 suka shiga baitul mali wasu kasashe dake nahiyar tsakanin shekara 2015-2019, yayin da bilyan 22 ya fita a zaman biyan bashi.

A halin da ake ciki kuma, an fara shari’ar tsohuwar ministan mai ta Najeriya Allison Madueke, ranar Talata, inda masu gabatar da kara suka ce ta karbi cin hanci da rashawa domin bada ayyukan kwangila ta fuskar Makamashi.

A gefe daya kuma, gwamnatin jihar Nija a Najeriya zata yi aiki da Bankin Islama domin habaka samarda makamashi ta rana, kan kudi dala milyan 163, domin kara samarda wutan lantarki da zai taimakawa ayyukan noma da masana’antu, kamar yadda jami’ai suka fada ranar talata.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure
Next Post: Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
An Kashe Sojojin Ukraine Dubu 55 A Kasar Rasha Afrika
Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Janet Ce Gwarzuwar ‘Yar Wasan Mako NWFL Wasanni
  • Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
  • Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.