Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC
Published: November 27, 2025 at 7:14 PM | By: Nafisa Ahmad

Wani dan bindiga ya bude wuta ya harbi wasu dakarun tsaron cikin gida su biyu daga Jihar West Virginia da aka girka a nan Washington DC, dab da fadar White House, a wani lamarin da magajiyar garin birnin Washington ta bayyana a zaman hari na gangan a kan sojojin.

Darektan hukumnar binciken manyan laifuffuka ta tarayya, Kash Patel, da magajiyar garin birnin Washington, Muriel Bowser, sun ce dakarun suna kwance a asibiti, rai a hannun Allah.

Irin wannan farmaki na ba-saban ba a kan dakarun tsaron cikin gida yana zuwa a daidai lokacin da ake ta ci gaba cacar baki kan girka irin wadannan dakaru a nan Washington da wasu birane, inda aka yi wata da watanni ana shigar da kararraki a kotuna da yin zaga-zanga kan yadda gwamnatin Trump take amfani da sojoji don takalar abinda ta kira matsalar aikata laifuffuka.

Shi ma wanda ake zargin cewa dan bindigar ne, an harbe shi kuma na kama shi, amma ana jin rauninsa ba mai tsanani ba ne.

Nan da nan gwamnatin Mr. Trump ta bada umurnin da a kara turo karin dakarun tsaron cikin gida dari biyar (500) zuwa nan Washington.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka
Next Post: ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji Labarai
Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
  • Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.