Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela
Published: December 17, 2025 at 4:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Trump na Amurka ya bada umurnin a tare dukkan jiragen ruwan dakon mai da aka sanya ma takunkumi a hana su shiga Venezuela, a wani matakin da ake dauka a zaman karin matsin lamba a kan shugaba Nicolas Maduro da kuma takura tattalin arzikin kasar.

Wannan umurni na shugaba Trump yana zuwa a bayan da sojojin Amurka suka kama wani jirgin ruwan jigilar man fetur a makon da ya shige a kusa da gabar kasar Venezuela, a bayan da Amurka ta girka sojoji masu yawa a yankin.

A cikin bayanin da yayi a shafinsa na sada zumunta ranar talata, shugaba Trump yayi zargin cewa Venezuela tana amfani da kudin mai wajen karfafa safarar muggan kwayoyi da wasu laifuffukan, yana mai lasar takobin ci gaba da matsin lambar soja har sai kasar Venezuela ta mayar ma Amurka a cewarsa Mai da kasa da kuma kadarorinta.

Abinda ba a fahimta a wannan bayani na shugaban ba shine wane irin hakki Amurka take da shi a game da man fetur ko kasa ko kuma kadara na Venezuela.

Shugaba Nicolas Maduro ya yaba ma ‘yan kasarsa da yace an shafe makonni 25 ana neman firgita su da nuna musu yatsa.

Trump yace duk wannan matsin da ake yi na neman hana safarar muggan kwayoyi zuwa Amurka ne, amma kuma shugabar ma’aikatan sa Susie Wiles ta fada cikin wata hirar da aka wallafa ranar talata a mujallar Vanity cewa wannan matsi wani yunkuri ne na kawar da shugaba Maduro daga kan mulki.

Kasar venezuela ta fi kowace kasa a duniya arzikin man fetur.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba
Next Post: Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya Afrika
Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika
Amurka Tasakawa Sojin Rwanda Takunkumi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.