Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela
Published: December 17, 2025 at 4:40 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Trump na Amurka ya bada umurnin a tare dukkan jiragen ruwan dakon mai da aka sanya ma takunkumi a hana su shiga Venezuela, a wani matakin da ake dauka a zaman karin matsin lamba a kan shugaba Nicolas Maduro da kuma takura tattalin arzikin kasar.

Wannan umurni na shugaba Trump yana zuwa a bayan da sojojin Amurka suka kama wani jirgin ruwan jigilar man fetur a makon da ya shige a kusa da gabar kasar Venezuela, a bayan da Amurka ta girka sojoji masu yawa a yankin.

A cikin bayanin da yayi a shafinsa na sada zumunta ranar talata, shugaba Trump yayi zargin cewa Venezuela tana amfani da kudin mai wajen karfafa safarar muggan kwayoyi da wasu laifuffukan, yana mai lasar takobin ci gaba da matsin lambar soja har sai kasar Venezuela ta mayar ma Amurka a cewarsa Mai da kasa da kuma kadarorinta.

Abinda ba a fahimta a wannan bayani na shugaban ba shine wane irin hakki Amurka take da shi a game da man fetur ko kasa ko kuma kadara na Venezuela.

Shugaba Nicolas Maduro ya yaba ma ‘yan kasarsa da yace an shafe makonni 25 ana neman firgita su da nuna musu yatsa.

Trump yace duk wannan matsin da ake yi na neman hana safarar muggan kwayoyi zuwa Amurka ne, amma kuma shugabar ma’aikatan sa Susie Wiles ta fada cikin wata hirar da aka wallafa ranar talata a mujallar Vanity cewa wannan matsi wani yunkuri ne na kawar da shugaba Maduro daga kan mulki.

Kasar venezuela ta fi kowace kasa a duniya arzikin man fetur.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba
Next Post: Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika
Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka Amurka
Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
  • Indiya Da Brazil Sun Kulla Yarjejeniyar Cinikayya Afrika
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.