Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka
Published: March 2, 2026 at 7:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yakin da Isar’ila da Amurka suke fafatawa da kasar Iran ya ci gaba ya kara tsamari a ranar Litinin, kuma ba’a ga alamar karshen sa ba. Isra’ila ta kaiwa kasar Lebanon hari, tana mai da martani ga harin da kungiyar Hezbollah suka kai mata.

Ita kuwa fadar Tehran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuki na drone zuwa kasashen tekun fasha, da filin sansanin sojin sama na Bahrain, har can zuwa kasar Cyprus.

Kasar Kuwait kuwa ta harbo jiragen yakin Amurka bisa kuskure, dukkanin mutane 6 na cikin jiragen sun tsira da ran su. Wani hoton bidiyo da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya yarda da sahihancin sa ya nuna daya daga cikin jiragen yana yin kasa yayin da injin sa ke kamawa da wuta.

Har ila yau Amurkan ta ce Sojojin ta 4 sun mutu, amma bata bada bayanin ta yadda suka rasa rayukan nasu ba. Wasu jami’an Amurka su biyu sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa mutane 3 na farko da suka rasu an kashe su ne a sansanin soji a Kuwait.

Shugaban Amurka Donald Trump ya ci gaba da kira ga ‘yan kasar Iran da su tashi su hambarar da shugabannin su, kuma ya ce harin da ake kaiwa zai iya shafe makonni. Su kuma shugabanni addini na Iran basu nuna wata alama ta yada Makamai ba.

Wani malamin makaranta a Iran Morteza Sedighi da ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters ta wayar tarho ya ce harin Amurka da Isra’ila yana kakkashe yara, kuma suna kai hari asibitoci, yace wannan shine demokradiyar da Trump yake so ya kawo mana. Farko hukumomin Iran sun kashe mutanen da basu ji ba basu gani ba, yanzu kuma Isra’ila da Amurka na kashe mutane inji shi.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci
Next Post: Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
An Kama Wani Da Abubuwan Fashewa A Zamfara Najeriya
Amurka Ta Kakaba Takunkumi Ga Kwamandojin Yakin Kasar Sudan Sauran Duniya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
  • Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
  • Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.