Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka
Published: March 2, 2026 at 7:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yakin da Isar’ila da Amurka suke fafatawa da kasar Iran ya ci gaba ya kara tsamari a ranar Litinin, kuma ba’a ga alamar karshen sa ba. Isra’ila ta kaiwa kasar Lebanon hari, tana mai da martani ga harin da kungiyar Hezbollah suka kai mata.

Ita kuwa fadar Tehran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuki na drone zuwa kasashen tekun fasha, da filin sansanin sojin sama na Bahrain, har can zuwa kasar Cyprus.

Kasar Kuwait kuwa ta harbo jiragen yakin Amurka bisa kuskure, dukkanin mutane 6 na cikin jiragen sun tsira da ran su. Wani hoton bidiyo da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya yarda da sahihancin sa ya nuna daya daga cikin jiragen yana yin kasa yayin da injin sa ke kamawa da wuta.

Har ila yau Amurkan ta ce Sojojin ta 4 sun mutu, amma bata bada bayanin ta yadda suka rasa rayukan nasu ba. Wasu jami’an Amurka su biyu sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa mutane 3 na farko da suka rasu an kashe su ne a sansanin soji a Kuwait.

Shugaban Amurka Donald Trump ya ci gaba da kira ga ‘yan kasar Iran da su tashi su hambarar da shugabannin su, kuma ya ce harin da ake kaiwa zai iya shafe makonni. Su kuma shugabanni addini na Iran basu nuna wata alama ta yada Makamai ba.

Wani malamin makaranta a Iran Morteza Sedighi da ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters ta wayar tarho ya ce harin Amurka da Isra’ila yana kakkashe yara, kuma suna kai hari asibitoci, yace wannan shine demokradiyar da Trump yake so ya kawo mana. Farko hukumomin Iran sun kashe mutanen da basu ji ba basu gani ba, yanzu kuma Isra’ila da Amurka na kashe mutane inji shi.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci
Next Post: Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
Duk Da Rauni Daya Samu Sakamakon Hari Mojtaba Khameni Yafara Aiki Labarai
Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa Siyasa
  • Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
  • Iran Zata Sassauta Shirin Nukiliya Tsakaninta Da Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
  • Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.