Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Ga Alamu Jakuna Za Su Bace A Doron Kasa Nan Da Shekaru 5
Published: December 9, 2025 at 4:24 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Hukumar kula da rayuwar dabbobi ta majalisar dinkin duniya da masu kare hakkin dabbobi na Afurka sun nuna damuwa ga yanda Jakuna ke matukar raguwa a duniya, saboda kashe su da a ke yi don samun nama da kuma amfani da fatar su wajen magani da ‘yan kasar Sin ke amfani da shi.

A gaba daya duniya alkaluma da aka yi amfani da wata na’ura, na nuni da cewar akwai kimanin Jakuna miliyan 40 a doron kasa.

Lamarin ya ta’azzara bayan ‘yan kasar Sin sun zuba jarin fataucin Jakuna a Najeriya don amfani da fatar Jakin.

Hakan ya haddasa tashin gauron zabi na jakuna da kuma barazanar karar da su har da rahoton shigo da naman bayan sayar da fatar Abuja a soyawa jama’a a matsayin naman yau da kullum.

Tsohon dan majalisar wakilan Najeriya mai sha’awar lamuran kare dabbobi daga cutarwa, Garba Datti Muhammad, ya ce nan da shekara 5 matukar ba a dau matakan da su ka dace ba, Jakuna za su kare a duniya.

Garba Datti wanda ya gabatar da babban jawabi a taron hukumar kula da dabbobi ta majalisar dinkin duniya da ta Afurka, ya ce wasu kan yanka jakuna don amfani da fatar ko cin naman maimakon amfani da jakunan ga lamuran sufuri a karkara.

Datti ya kara da cewa yanzu a duk duniya kimanin Jakuna miliyan 40 a ke da su kuma a na cigaba da hallaka su da cutar da su ba tare da kula da lafiyar su ko gudunmawar da su ke bayarwa ga tattalin arziki ba.

Game da barazanar sayarwa jama’a naman da a ka haramta yankawa na jakuna, wasu manyan makiyaya sun fara tunanin bude mayankar zamani a manyan biranen Najeriya.

Isa Tafida Mafindi tuni ya kafa irin wannn mayankar da ta lashe Naira miliyan dubu goma sha biyar.

Wani abun takaici shi ne yanda mutane ke barin jakuna su hau manyan hanyoyi da dare da kwatsam mai tuka mota sai ya yi kicibis da jaki a tsakiyar titi da kan haddasa mummunan hatsari.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/AS-DONKEYS-SEEM-TO-ON-VERGE-OF-EXTERMINATION-1.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Tura Sojoji Benin
Next Post: Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.