Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware
Published: December 27, 2025 at 9:24 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar hadin kai da Saudiyya take yiwa jagoranci a Yemen tace zata maida martani kan duk wani yunkurin da ‘yan aware dake kudancin lardin Hadaramount suka yi, wadda ka iya illa ga kokarin tsagaita wuta kamar yadda Kamfanin dilancin labarai na Saudiyya ya bayyana a yau Asabar.

Sanarwar da kakakin rundunar hadin guiwa Janar Turki al-Maliki ya bayar, ya biyo bayan bukatar da shugaban majalisar gudanarwa a Yemen,Rashad al-Alimi yayi na daukar matakan gaggawa domin kare farar hula a lardin Hadaramount bayanda mayaka wadanda suke da alaka da kungiyar ‘yan tawaye da ake yiwa lakabi da STC suka keta yarjejenyar da take aiki na tsagaita wuta

Kungiyar ‘yan tawayen STC watau Southern Transitional Council da turanci, wacce hadaddiyar daular larabawa take marawa baya, ta hambare gwamnatin yankin da Saudiyya da kuma kasashen duniya suka amince data ita a farkon watan nan daga helkwatarta dake Aden, kuma ta ayyana iko a duk fadin kudancin kasar.

A ranar Jumma’a dai kunigyar ta STC tayi watsi da kiran da Saudiyya tayi mata cewa ta janye daga sassan data kama a farkon watan nan, tana mai cewa zata ci gaba da aikin mamaye lardunan dake kudancin Yemen da ake kira Hadaramount da Mahra.

Daga bisani anji ministan tsaron Saudiyya Yerima Khalid Bin Salman, ta wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, yana kira ga Kungiyar ta STC ta saurari kokarin sulhu da ake yi, kuma ta amince da a gudanar da shawarwari da nufin shawo kan rikici a yankin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Next Post: Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta

Karin Labarai Masu Alaka

Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
Sojojin Isra’ila Sun Kashe Babban Kwamandan Kungiyar Hezbollah Afrika
Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika
Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
  • Matar El-Rufai Ta Roƙi Tinubu Ya Tabbatar An Yi Wa Mijinta Adalci Afrika
  • Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
  • Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
  • An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.