Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Published: December 27, 2025 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Najeriya tace harin da Amurka ta kai ta sama wadda take goyon bayansa matakin ya afkawa sansanonin ‘yan bindigar ISIS guda biyu a dajin da ake kira Bauni dake jihar Sokoto, inda ta auna mayaka daga ketare wanda suke shiga Najeriya daga yankin Sahel.

Farmakin da aka kai ranar Alhamis, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince dashi, wadda aka kaddamar daga sasanonin Amurka na ruwa daga gabar da teku da ake kira Gulf a Guniea, bayan wani lokaci mai tsawo ana tattara bayanan sirri, da tsare tsare, kamar yadda ma’aikatar yada labarai ta Najeriya ta bada sanarwa a ranar jumma’a.

Adadin makamai 16 masu aiki da GPS aka yi amfani da su, wadda suka yi nasarar gamawa da mayakan ISIS wadanda suke kokarin kutsawa cikin Najeriya daga yankin na Sahel, inji hukumomin Najeriya.

Bayanan sirri sun nuna cewa, mayakan kungiyar ISIS daga waje ne suke amfani da sansanoni tare da hadin guiwar wasu kungiyoyin mayaka daga cikin gida inda suke shirya kai munanan hare hare, kamar yadda sanarwar tayi karin bayani.

Ta kara da cewa harin bai rutsa da farar hula ba, koda shike baragusai sun fada kan wasu garuruwa a jihohin Sokoto da kwara.

Farmakin da Amurkan ta kai ya nuna hadin kan tsaro na ba sabon ba tsakanin hukumomi a Abuja da Washington, ganin yadda tashe-tashen hankula da ake alakantawa da addinin Musulunci suke kara bazuwa zuwa a kudanci daga yankin Sahel.

Gwamnatin Najeriya tace a shirye take ta ci gaba da daukar matakai na kare rayuka da dukiyoyin al’umarta, yayinda shugaba Trump na Amurka yace a shirye Washington take ta kai karin wasu hare hare.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji
Next Post: Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware

Karin Labarai Masu Alaka

Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
  • Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar Hakar Ma’adanai A Kasar Zambiya Ta Dakatar Da Ayyukanta Kimiya
  • Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika
  • Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
  • Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
  • Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.