Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto
Published: December 27, 2025 at 9:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Najeriya tace harin da Amurka ta kai ta sama wadda take goyon bayansa matakin ya afkawa sansanonin ‘yan bindigar ISIS guda biyu a dajin da ake kira Bauni dake jihar Sokoto, inda ta auna mayaka daga ketare wanda suke shiga Najeriya daga yankin Sahel.

Farmakin da aka kai ranar Alhamis, shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya amince dashi, wadda aka kaddamar daga sasanonin Amurka na ruwa daga gabar da teku da ake kira Gulf a Guniea, bayan wani lokaci mai tsawo ana tattara bayanan sirri, da tsare tsare, kamar yadda ma’aikatar yada labarai ta Najeriya ta bada sanarwa a ranar jumma’a.

Adadin makamai 16 masu aiki da GPS aka yi amfani da su, wadda suka yi nasarar gamawa da mayakan ISIS wadanda suke kokarin kutsawa cikin Najeriya daga yankin na Sahel, inji hukumomin Najeriya.

Bayanan sirri sun nuna cewa, mayakan kungiyar ISIS daga waje ne suke amfani da sansanoni tare da hadin guiwar wasu kungiyoyin mayaka daga cikin gida inda suke shirya kai munanan hare hare, kamar yadda sanarwar tayi karin bayani.

Ta kara da cewa harin bai rutsa da farar hula ba, koda shike baragusai sun fada kan wasu garuruwa a jihohin Sokoto da kwara.

Farmakin da Amurkan ta kai ya nuna hadin kan tsaro na ba sabon ba tsakanin hukumomi a Abuja da Washington, ganin yadda tashe-tashen hankula da ake alakantawa da addinin Musulunci suke kara bazuwa zuwa a kudanci daga yankin Sahel.

Gwamnatin Najeriya tace a shirye take ta ci gaba da daukar matakai na kare rayuka da dukiyoyin al’umarta, yayinda shugaba Trump na Amurka yace a shirye Washington take ta kai karin wasu hare hare.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji
Next Post: Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dusar Kankara Ta Hana Jirage Tashi A Birnin Paris Labarai
  • Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • An Kashe Sojojin Ukraine Dubu 55 A Kasar Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.