Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya
Published: July 22, 2026 at 5:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa abin da ya bayyana a matsayin jajircewarsa wajen jagorantar Najeriya da kuma ƙoƙarin magance matsalolin tsaro, musamman hare-haren da ke shafar wasu al’ummomin Kiristoci.

A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 6 ga Yulin 2026 da ya aike wa Shugaba Tinubu, Trump ya yaba da ƙudurin shugaban na yaƙi da ta’addanci tare da tabbatar da cewa Amurka za ta ci gaba da mara wa Najeriya baya wajen inganta tsaro da tabbatar da zaman lafiya.

Trump ya ce abin alfahari ne gare shi ya tsaya tare da Shugaba Tinubu wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, yana mai bayyana cewa haɗin gwiwar ƙasashen biyu zai taimaka wajen ƙarfafa Najeriya da bunƙasa tattalin arzikinta.

Shugaban na Amurka ya ce Najeriya da Amurka suna da manufar bai ɗaya ta yaƙi da ta’addanci a yankin Yammacin Afirka, yana mai nuni da cewa Tsarin Haɗin Gwiwar Tsaro na Amurka da Najeriya na shekarar 2026 ya samar da ingantaccen tubali na zurfafa haɗin gwiwar soji tsakanin ƙasashen biyu.

Ya kuma bayyana cewa Amurka ta tura jami’an rundunar musamman domin horas da sojojin Najeriya tare da ba su ƙwarewa, bayanan sirri da sauran tallafin da za su taimaka wajen yaƙi da ta’addanci da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Trump ya kuma bayyana fatan ci gaba da tattaunawa da Shugaba Tinubu domin ƙara bunƙasa alaƙar da ke tsakanin Najeriya da Amurka.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe
Next Post: Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
  • Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
  • Dan Wasan Baya Na Chelsea, Disasi, Zai Yi Gwajin Lafiyarsa A Crystal Palace Wasanni
  • Oliseh, Ya Ba Eric Chelle, Shawara Da Ya Zamo Mai Tsauri AFCON 2025. Wasanni
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
  • Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.