Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya
Published: July 22, 2026 at 5:05 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa abin da ya bayyana a matsayin jajircewarsa wajen jagorantar Najeriya da kuma ƙoƙarin magance matsalolin tsaro, musamman hare-haren da ke shafar wasu al’ummomin Kiristoci.

A cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 6 ga Yulin 2026 da ya aike wa Shugaba Tinubu, Trump ya yaba da ƙudurin shugaban na yaƙi da ta’addanci tare da tabbatar da cewa Amurka za ta ci gaba da mara wa Najeriya baya wajen inganta tsaro da tabbatar da zaman lafiya.

Trump ya ce abin alfahari ne gare shi ya tsaya tare da Shugaba Tinubu wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, yana mai bayyana cewa haɗin gwiwar ƙasashen biyu zai taimaka wajen ƙarfafa Najeriya da bunƙasa tattalin arzikinta.

Shugaban na Amurka ya ce Najeriya da Amurka suna da manufar bai ɗaya ta yaƙi da ta’addanci a yankin Yammacin Afirka, yana mai nuni da cewa Tsarin Haɗin Gwiwar Tsaro na Amurka da Najeriya na shekarar 2026 ya samar da ingantaccen tubali na zurfafa haɗin gwiwar soji tsakanin ƙasashen biyu.

Ya kuma bayyana cewa Amurka ta tura jami’an rundunar musamman domin horas da sojojin Najeriya tare da ba su ƙwarewa, bayanan sirri da sauran tallafin da za su taimaka wajen yaƙi da ta’addanci da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Trump ya kuma bayyana fatan ci gaba da tattaunawa da Shugaba Tinubu domin ƙara bunƙasa alaƙar da ke tsakanin Najeriya da Amurka.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe
Next Post: Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Jarida Saleh Shehu Ashaka Rasuwa Labarai
  • Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
  • Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya Labarai
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2 Sauran Duniya
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.