Morocco ta kwashe mutane fiye da dubu hamsin daga birnin Kasar el-Kabir, kusan rabin mazauna birnin sakamakon barazanar ambaliyar ruwa, biyo bayan ruwan sama kamar da bakin kwariya da aka yi makonni ana yi a yankin, kamar yadda kafofin yada labaran kasar suka fada jiya Litinin.
“Birnin ya zama kufayi,” kamar yadda mazauna garin Hicham Ajttou ya gayawa kamfanin dilancin labarai na Reuters, ta woyar tarho. “Kasuwanni da kantuna duka suna rufe, kuma galibin mazauna birnin walau sun bari gari bisa radin kansu, ko kuma an kwashe su.”
Cikin wasu dalilai da suka haddasa ambaliyyar ruwan da jami’an kasar suka bayar harda sako ruwa daga madatsan ruwa da bashi da nisa da birnin wanda ya cika makil.
Sojojin kasar sun tura wata tawagar mayaka da suka kware ta fuskar ayyukan ceto, da manyan motoci da kwararru ta fuskar kiwon lafiya, wadanda suke taimakawa a ayyuakn ceto da motocin da za’a kwashe su da su.
Ruwan sama kamar da bakin kwarya, ya kawo karshen fari na shekaru bakwai da kasar ta fuskanta.


