Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai

Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
Published: April 22, 2026 at 8:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da fitar da kudi naira biliyan 17 domin gudanar da wani babban shiri na samar da ci gaba a matakin mazabu (Wards) da ke faɗin ƙasar nan.

​Wannan tallafi, wanda aka yi wa laƙabi da “Community-Based National Social Action Fund”, an kafa shi ne domin taba rayuwar talakawa kai-tsaye a dukkanin mazabu 8,804 na Najeriya, ta hanyar ba su damar gudanar da ayyukan da suka fi damunsu a yankunansu.

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Lafiya da Walwalar Jama’a ta Tarayya ta fitar ranar Laraba, wadda mataimakin daraktan yaɗa labarai, Ado Bako ya sanya wa hannu, an bayyana cewa kowace mazaba za ta haɗa gwiwa ne da ƙungiyoyin sa-kai na cikin gida (CBOs) domin gano ayyukan da suka fi buƙata.

​Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya bayyana cewa wannan sabon salo ne na mika mulki ga talakawa. Ya ce, “Wannan tsari ya sanya al’umma a gaba wajen neman ci gaba. Ta hanyar barin kowace mazaba ta zaɓi abin da ya fi damunta, muna buɗe hanyoyin samar da maslaha da za su inganta rayuwa da kuma ayyukan gwamnati a inda aka fi buƙata.”

Sanarwar ta nuna cewa za a kashe kuɗaɗen ne a fannonin da suka haɗa da​Samar da abinci mai gina jiki ga al’umma, ​Samar da magunguna da kayayyakin kiwon lafiya, ​Gyaran makarantu, asibitoci, da samar da tsarin tsaftar muhalli.

​An tsara cewa za a fara aiwatar da wannan shiri ne daga ranar 1 ga watan Maris, 2026 zuwa watan Disambar 2026, inda Ma’aikatar Kuɗi da Ofishin Akanta-Janar na Ƙasa za su kula da asusun da aka ware wa shirin.

A wani labarin kuma mai alaƙa da wannan, Shugaba Tinubu ya amince da ɗaga matsayin Cibiyar Horar da Masu Maganin Kanjamau da Kuturta ta Ƙasa (NTBLTC) da ke Zariya, zuwa matsayin Babbar Cibiyar Bincike da Kula Lafiyar Jama’a da Cututtuka Masu Yaduwa (National Institute of Public Health and Infectious Diseases).

​Wannan mataki na nufin mayar da cibiyar ta Zariya ta zama tungar bincike, horarwa, da kuma shirin taryar duk wata annoba ko barazanar cututtuka da ka iya ɓallowa a ƙasar nan.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa
Next Post: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Tace Jakadan Kasar Ta A Lebanon Zai Cigaba Da Zama A Beirut Afrika
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya
  • Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa
  • Gwamnatin Filato Ta Gurfanar Da Maharan Rukuba A Kotu
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Chadi Ta Sauyawa ‘Yan Gudun Hijira Matsuguni Afrika
  • An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka
  • Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka Sauran Duniya
  • Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
  • Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa Siyasa
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
  • Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.