Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka
Published: February 6, 2026 at 10:43 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar talatar makon nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya sanya hanu na kara wa’adin cinikayya tsakanin Amurka da kasashen Afirka ba tare da haraji ba da ake kira AGOA, na tsawon shekara daya, zuwa 31 ga watan Disamba shekara ta 2026.

Kara tsawon wa’adin ya kawo karshen zaman zullumi game da makomar shirin, yayinda kasashen duniya suke ji da matsanancin haraji da shugaban na Amurka ya azawa kasashen duniya ranar 2 ga watan Afrilun bara. Karewar wa’adin cinikayyar da ake kira AGOA ya jefa dubban ayyuka a nahiyar Afirka cikin hadari.

Kasar Lesotho, kasar Afirka da ta fi ko wacce dogaro kan kayayyaki da take sayarwa a kasuwannin Amurka, tsawaita wa’adin, ya sassauta zaman zullumi, ko da shike rashin tabbas din har yanzu yana nan.

“Ina da kwarin guiwar za’a sami wani abu na lokaci mai tsawo,” inji ministan harkokin kasuwanci na Lesotho Mokheti Shelile a hirar da yayi da kamfanin dillancin labarai na Reuters ofishinsa. Ya kara da cewa karin wa’adin na shekara daya bai dace da yanayin harkokin cinikayyar kasarsa ba. Bangaren sake-sake shine kan gaba na kayayyaki da Lesotho take sayarwa a kasashen ketare.

A watan Afrilun bara Amurka ta dorawa Lesotho harajin kashi 50 cikin dari, daga bisani gwamnatin Trump ta rage shi zuwa kashi 15 cikin dari, duk da haka wannan harajin yana da nauyi ga Lesotho wacce ta dogara kan cinikin kayayyakin sawa da Amurkawa suke saye.

Afrika, Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar
Next Post: Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa

Karin Labarai Masu Alaka

APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu Afrika
  • An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
  • Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.