Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka
Published: February 6, 2026 at 10:43 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar talatar makon nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya sanya hanu na kara wa’adin cinikayya tsakanin Amurka da kasashen Afirka ba tare da haraji ba da ake kira AGOA, na tsawon shekara daya, zuwa 31 ga watan Disamba shekara ta 2026.

Kara tsawon wa’adin ya kawo karshen zaman zullumi game da makomar shirin, yayinda kasashen duniya suke ji da matsanancin haraji da shugaban na Amurka ya azawa kasashen duniya ranar 2 ga watan Afrilun bara. Karewar wa’adin cinikayyar da ake kira AGOA ya jefa dubban ayyuka a nahiyar Afirka cikin hadari.

Kasar Lesotho, kasar Afirka da ta fi ko wacce dogaro kan kayayyaki da take sayarwa a kasuwannin Amurka, tsawaita wa’adin, ya sassauta zaman zullumi, ko da shike rashin tabbas din har yanzu yana nan.

“Ina da kwarin guiwar za’a sami wani abu na lokaci mai tsawo,” inji ministan harkokin kasuwanci na Lesotho Mokheti Shelile a hirar da yayi da kamfanin dillancin labarai na Reuters ofishinsa. Ya kara da cewa karin wa’adin na shekara daya bai dace da yanayin harkokin cinikayyar kasarsa ba. Bangaren sake-sake shine kan gaba na kayayyaki da Lesotho take sayarwa a kasashen ketare.

A watan Afrilun bara Amurka ta dorawa Lesotho harajin kashi 50 cikin dari, daga bisani gwamnatin Trump ta rage shi zuwa kashi 15 cikin dari, duk da haka wannan harajin yana da nauyi ga Lesotho wacce ta dogara kan cinikin kayayyakin sawa da Amurkawa suke saye.

Afrika, Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar
Next Post: Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa

Karin Labarai Masu Alaka

Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.