Sakamakon wacin gadi da aka bayar na zaben shugaban kasa a Guinea-Conakry ya nuna cewa madugun juyin mulki Mamady Doumbouya, shine ya lashe zaben da gagarumin rinjaye
Sakamakon na wucin gadi da aka sanar ranar talata ya nuna cewa Doumbouya ya samu kusan kashi 87 daga cikin 100 na kuri’un da aka jefa ran 28 ga watan nan na Disamba, rinjayen da ya sa ba ma sai an sake zaben fitar da gwani ba.
Kotun kolin kasar tana da kwanaki 8 domin tabbatarwa ko kin tabbatar da wannan sakamako idan an samu wanda zai kalubalance shi.
Da ma dai ana sa ran Doumbouya zai lashe wannan zabe da zai ba shi wa’adin shekaru 7 a kan kujerar shugabancin kasar.
Tsarin mulki na farko da aka bayar a kasar Guinea Conakry a bayan juyin mulkin Doumbouya na 2021, ya haramtawa shugabannin sojoji tsayawa takara a zaben, amma a watan Satumba an gudanar da kuri’ar raba gardama a kan wani tsarin mulkin wanda yayi watsi da wannan tanadi.
Kasar Guinea-Conakry ta fi kowace kasa a duniya arzikin karfen goran ruwa da kuma bakin karfe.


