Kasashen Mali da Burkina Faso sun ba da sanarwa da maraicen talatar nan cewa zasu haramtawa Amurkawa shiga cikin kasashensu, domin maida martani ga matakin da shugaba Donald Trump ya dauka na haramtawa ‘yan kasashen biyu shiga kasar Amurka.
Wannan matakin da ministocin harkokin wajen kasashen biyu suka bayar da sanarwarsa a lokuta daban daban, ya nuna irin yadda dangantaka ta yi tsami a tsakanin gwamnatocin mulkin soja na kasashen Afirka ta Yamma da kuma Amurka.
A ranar 16 ga watan Disamba ne shugaba Trump ya fadada takunkumin hana wasu ‘yan kasashen waje izinin shiga Amurka inda ya hada da kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Nijar, wadanda gwamnatocin su suka balle daga Kungiyar ECOWAS ko CDEAO suka kafa ta su ta Kungiyar Kasashen Yankin Sahel.
Tun da fari, gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta bada sanarwar daukar irin wannan matakin ramawa kura aniyarta, ta ce ta haramtawa dukkan Amurkawa shiga cikin kasarta.


