Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen
Published: December 31, 2025 at 5:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasashen Mali da Burkina Faso sun ba da sanarwa da maraicen talatar nan cewa zasu haramtawa Amurkawa shiga cikin kasashensu, domin maida martani ga matakin da shugaba Donald Trump ya dauka na haramtawa ‘yan kasashen biyu shiga kasar Amurka.

Wannan matakin da ministocin harkokin wajen kasashen biyu suka bayar da sanarwarsa a lokuta daban daban, ya nuna irin yadda dangantaka ta yi tsami a tsakanin gwamnatocin mulkin soja na kasashen Afirka ta Yamma da kuma Amurka.

A ranar 16 ga watan Disamba ne shugaba Trump ya fadada takunkumin hana wasu ‘yan kasashen waje izinin shiga Amurka inda ya hada da kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Nijar, wadanda gwamnatocin su suka balle daga Kungiyar ECOWAS ko CDEAO suka kafa ta su ta Kungiyar Kasashen Yankin Sahel.

Tun da fari, gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta bada sanarwar daukar irin wannan matakin ramawa kura aniyarta, ta ce ta haramtawa dukkan Amurkawa shiga cikin kasarta.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry
Next Post: An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya

Karin Labarai Masu Alaka

An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika
APC Ta Sauya Jerin ‘Yan Takararta Bayan Nazarin Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Fidda Gwani Afrika
Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika
Prime Ministar Italiya Ta Ziyarci Saudi Arabia Afrika
Tinubu Zai Gabatar Da Jawabi ga Shugabannin Duniya A Taron UNGA Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika
  • Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
  • Shugaba Trump Ya Jinjinawa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya Afrika
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
  • Kyaftin Na Super Eagles Ya Yi Ritaya. Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.