Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen
Published: December 31, 2025 at 5:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasashen Mali da Burkina Faso sun ba da sanarwa da maraicen talatar nan cewa zasu haramtawa Amurkawa shiga cikin kasashensu, domin maida martani ga matakin da shugaba Donald Trump ya dauka na haramtawa ‘yan kasashen biyu shiga kasar Amurka.

Wannan matakin da ministocin harkokin wajen kasashen biyu suka bayar da sanarwarsa a lokuta daban daban, ya nuna irin yadda dangantaka ta yi tsami a tsakanin gwamnatocin mulkin soja na kasashen Afirka ta Yamma da kuma Amurka.

A ranar 16 ga watan Disamba ne shugaba Trump ya fadada takunkumin hana wasu ‘yan kasashen waje izinin shiga Amurka inda ya hada da kasashen Mali da Burkina Faso da kuma Nijar, wadanda gwamnatocin su suka balle daga Kungiyar ECOWAS ko CDEAO suka kafa ta su ta Kungiyar Kasashen Yankin Sahel.

Tun da fari, gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta bada sanarwar daukar irin wannan matakin ramawa kura aniyarta, ta ce ta haramtawa dukkan Amurkawa shiga cikin kasarta.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry
Next Post: An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya

Karin Labarai Masu Alaka

Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
Akwai Yiwuwar Shugaban Ƙasar Afirka Ta Tsakiya Touadera Yasamu Nasara A Karo Na Uku Afrika
Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi Afrika
Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka Wasanni
  • An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.