Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Published: December 7, 2025 at 4:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 7, 2025

‘Yan bindiga sun hallaka Malaman makaranta a gundumar Filingue da ke yankin Tilabery iyakar Nijar da Mali.
Lamarin ya tada hankulan uwar kungiyar malaman makaranta wace ta yi kiran hukumomi su tsaurara matakai a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro donganin an ci gaba da karantarwa a makarantun boko.
Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a lokacin da wadanan malamai da suka hada da darektan makarantar kauyen Sabon garin Takoussa Abdoulaye Askou da takwaransa na makarantar kauyen Maitalakia Nouhou Oumarou na kan hanyar zuwa taron kwamitin COGES da aka gudanar a Filingue lokacin da maharan suka afka masu kamar yadda kungiyar malaman kwantaragi ta SYNACEB ta bayyana a sanarwar nuna juyayi da ta fitar.
Wannan ba shi ne karon farko da ‘yan bindiga ke far wa malaman makaranta ba kokuma dakunan karantun da kansu a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro sabili kenan SYNACEB ke tunar da mahakunta a kan bukatar karfafa matakai domin dorewar sha’anin ilimi.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnati a kan wannan al’amari. Na tuntubi mai bai wa ministar ilimi shawara Issoufou Arzika ta waya to amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza Issa wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kira ta sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
Yankin Tilabery mai iyaka da Burkina Faso da Mali na daga cikin yankuna mafi fama da barazanar ‘yan bindiga lamarin da tun a wajejen 2017 ya haddasa rufe makarantu da dama koda ya ke a Watan satumban da ya gabata ministar ilimi Dr Elizabeth Cherif ta sanar cewa yawan irin wadanan makarantu ya ragu.
To amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kirata sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
KISAN MALAMAN MAKARANTA
Afrika

Post navigation

Previous Post: ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji
Next Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade

Karin Labarai Masu Alaka

Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
Boko Haram Ta Kai Hari Maiduguri Cikin Dare Afrika
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Bukaci Al’ummar Gombe Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Ta’addanci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika
  • Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
  • Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.