Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery
Published: December 7, 2025 at 4:13 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 7, 2025

‘Yan bindiga sun hallaka Malaman makaranta a gundumar Filingue da ke yankin Tilabery iyakar Nijar da Mali.
Lamarin ya tada hankulan uwar kungiyar malaman makaranta wace ta yi kiran hukumomi su tsaurara matakai a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro donganin an ci gaba da karantarwa a makarantun boko.
Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a lokacin da wadanan malamai da suka hada da darektan makarantar kauyen Sabon garin Takoussa Abdoulaye Askou da takwaransa na makarantar kauyen Maitalakia Nouhou Oumarou na kan hanyar zuwa taron kwamitin COGES da aka gudanar a Filingue lokacin da maharan suka afka masu kamar yadda kungiyar malaman kwantaragi ta SYNACEB ta bayyana a sanarwar nuna juyayi da ta fitar.
Wannan ba shi ne karon farko da ‘yan bindiga ke far wa malaman makaranta ba kokuma dakunan karantun da kansu a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro sabili kenan SYNACEB ke tunar da mahakunta a kan bukatar karfafa matakai domin dorewar sha’anin ilimi.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnati a kan wannan al’amari. Na tuntubi mai bai wa ministar ilimi shawara Issoufou Arzika ta waya to amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza Issa wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kira ta sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
Yankin Tilabery mai iyaka da Burkina Faso da Mali na daga cikin yankuna mafi fama da barazanar ‘yan bindiga lamarin da tun a wajejen 2017 ya haddasa rufe makarantu da dama koda ya ke a Watan satumban da ya gabata ministar ilimi Dr Elizabeth Cherif ta sanar cewa yawan irin wadanan makarantu ya ragu.
To amma ya mayar da ni wajen jami’ar hulda da ‘yan jarida Hadiza wace ba ta daga wayarta ba lokacin da na kirata sannan ba ta amsa sakon text din da na tura ma ta har zuwa lokacin aika wannan rahoto.
KISAN MALAMAN MAKARANTA
Afrika

Post navigation

Previous Post: ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji
Next Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade

Karin Labarai Masu Alaka

Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda Afrika
Maulidi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Hutu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
  • 2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Al Hilal Ta Cimma Yarjejeniya Da Pedro Wasanni
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Arsenal Tana Ci Gaba Da Kokarin Dauko Morgan Rogers Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.