Da misalin ƙarfe 12:15am mazauna birnin Maiduguri su ka fara jin ƙarar fashewar wani abu mai kama da ƙarar bomb sabida ba bu wanda zai iya tabbatar wa amma daga bisani an hango jirgin Sojin saman Najeriya na shawagi a sararin samaniya.
Bayan tuntubar wasu mazauna Maidugurin, sun shaida cewa ana kyautata zaton cewa hari ne da ƴan ta’adda suka yi yunkurin kaddamar wa sai dai sun gamu da mayaƙan sojin saman Najeriya.
Harin ya jefa mazauna wasu unguwanni cikin firgici, sakamakon ƙarar harbe-harbe masu ƙarfi da ake ji a sassa daban-daban na birnin.
Unguwannin da abin ya shafa sun haɗa da Dala da Bulamari da kuma Ajilari Cross, inda rahotanni ke nuna cewa mazauna da dama sun tsere daga gidajensu domin neman mafaka yayin da lamarin ke ƙara tsananta.
Wasu mazauna unguwannin Dala da Bulamari sun shaida wa wakilinmu cewa sojoji sun mayar da martani tare da tallafin jirgin sojin sama sun kai ɗauki.


