Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai
Published: February 10, 2026 at 10:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 10, 2026

Yawan mai da kasashe dake kungiyar OPEC masu arzikin mai suke hakowa yayi kasa sakamakon karancin mai da Najeriya da Libya suke hakowa, kamar yadda wani bincike da kamfanin dillancin lbarai na Reuters ya gano Ranar Litinin.

Kasashe da suke cikin kungiyar OPEC suna hakar mai ganga milya 28.34 ako wace rana cikin watan Junairun da ya wuce, wanda ya nuna koma baya da kamar gangar mai dubu 60 idan aka duba alkaluman watan Disamba binciken ya nuna, Najeriya ce ta sami koma baya sosai a yawan abunda take hakowa.

OPEC da kasashe kawayenta da suka hada da Rasha sun fara rage hanu a watanni uku na farkon shekara na yawan mai da suke hakowa saboda fargabar suna iya fuskantar kwanten mai a duniya.

Karkashin wata yarjejeniyar da kasashe 8 da suke cikin kungiyar da wasu kawayenta ba zasu kara yawan abunda suke hakowa ba a watan jiya, sun hada da Aljeriya, da Iraq, da Kuwait, da saudi Arabia, da hadaddiyar daular larabawa, gabannin ganin tasirin rage abunda suke hakowa da adadinsa ya kai gangan dubu 130, da zai shafi Iraqi da kuma hadaddiyar daular larabawa.

Najeriya ce dai aka ga matukar koma bayan mai da take hakowa, da kuma Libya, wacce ta fuskanci matsalar yanayi wadda ya shafi lodin manta.

Haka nan an sami koma bayan mai daga Iran sosai, saboda Amurka tana kara mata takunkumi game da shirin Nukiliyar kasar.

Sai dai binciken bai fadi matsalar data sa Najeriya ta sami koma bayan mai da take hakowa ba.

A halinda ake ciki kuma, farashin mai ya tashi da kamar kashi daya, bayanda Amurka ta gargadi jiragen ruwa suyi taka tsantsan kusa da Iran.

Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC
Next Post: Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya Labarai
Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
Netanyahu: Zamu Kashe Dala Billiyan $110 Cikin Shekaru Hudu Don Kera Makamai Sauran Duniya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami Afrika
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.