Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai
Published: February 10, 2026 at 10:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 10, 2026

Yawan mai da kasashe dake kungiyar OPEC masu arzikin mai suke hakowa yayi kasa sakamakon karancin mai da Najeriya da Libya suke hakowa, kamar yadda wani bincike da kamfanin dillancin lbarai na Reuters ya gano Ranar Litinin.

Kasashe da suke cikin kungiyar OPEC suna hakar mai ganga milya 28.34 ako wace rana cikin watan Junairun da ya wuce, wanda ya nuna koma baya da kamar gangar mai dubu 60 idan aka duba alkaluman watan Disamba binciken ya nuna, Najeriya ce ta sami koma baya sosai a yawan abunda take hakowa.

OPEC da kasashe kawayenta da suka hada da Rasha sun fara rage hanu a watanni uku na farkon shekara na yawan mai da suke hakowa saboda fargabar suna iya fuskantar kwanten mai a duniya.

Karkashin wata yarjejeniyar da kasashe 8 da suke cikin kungiyar da wasu kawayenta ba zasu kara yawan abunda suke hakowa ba a watan jiya, sun hada da Aljeriya, da Iraq, da Kuwait, da saudi Arabia, da hadaddiyar daular larabawa, gabannin ganin tasirin rage abunda suke hakowa da adadinsa ya kai gangan dubu 130, da zai shafi Iraqi da kuma hadaddiyar daular larabawa.

Najeriya ce dai aka ga matukar koma bayan mai da take hakowa, da kuma Libya, wacce ta fuskanci matsalar yanayi wadda ya shafi lodin manta.

Haka nan an sami koma bayan mai daga Iran sosai, saboda Amurka tana kara mata takunkumi game da shirin Nukiliyar kasar.

Sai dai binciken bai fadi matsalar data sa Najeriya ta sami koma bayan mai da take hakowa ba.

A halinda ake ciki kuma, farashin mai ya tashi da kamar kashi daya, bayanda Amurka ta gargadi jiragen ruwa suyi taka tsantsan kusa da Iran.

Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC
Next Post: Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan

Karin Labarai Masu Alaka

Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
Tantance Gaskiyar Bayanai Shi Ne Ginshiƙin Aikin Jarida Mai Nagarta – Abdulaziz Afrika
Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya Labarai
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Gaddafi A Gidansa Dake Kasar Libya Afrika
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
  • An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.