Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC
Published: February 9, 2026 at 10:22 PM | By: Bala Hassan

Abdu Mai Kaba Ya Ajiye Aikin Horas da Wikki Tourist fc Bauchi da ke Arewa maso gabas a Najeriya.

Bayan da ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist fc Bauchi ta tashe canjaras da Katsina United 4-4 a wasan mako na 25 cikin gasar Firimiyar lig na Najeriya 25/26.

Ƙungiyar ta shiga rudani bisa irin maki da ta ke zubarwa a gida Wikki Tourist tayi canjaras a wasannin gida har guda 7 an shata a wasa daya a kakar wasan bana, jimillan makin da tayi a sara a gida 17, wadda hakan ya zamo babban kalu-bale a ƙungiyar kuma tana mataki na 15 da maki 29.

Inda wasu ki zargin maihoras da yanwasa Abdu Maikaba na rashin sanya Yan wasa a lokacin da ya dace, har ya kaima wasu magoya bayan Kulub din sukan fadi bakaken maganganu akan sa a zahiri da kuma shafin sada zumunta (Social media ) .na cin mutumcin sa

Saidai wasu masharhanta na gani cewa babu laifin Maikaba matsalar Wikki matsalace ta cikin gida, domin duk Shugaban da aka sauke yana da magoya baya da zasu tsangwami sabon shugaba suma a bangaren sabon babu shiri da wadda ya samesu a ciki musamman ƙungiyar Magoya baya saboda nan ta ke shima sabon shugaba zai sauke Jagororin magoya baya shima ya nada nasa wannan na daya daga cikin matsalolin Wikki ” inji masharhanta a jihar.

“Kuma anki ayi zaben Shuwagabannin magoya baya kamar yadda doka ya tanardar sai dai a bada rokon kwarya.

A gefe guda kuwa masu ruwa da tsaki akan harakar kwallon kafa a jihar wadda dasu aka kirkiri ƙungiyar sun daura laifine akan yadda aka sauka daga tsari da dokokin da aka kafa ƙungiyar.

Abdu Maikaba shi ya dawo da ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist zuwa buga gasar Firimiyar lig na Najeriya

Abdu Maikaba Ya Ajiya Aikinsa a Wikki Tourist
Ga abunda ya rubuta

 

 

 

 

 

 

 

“Ina so in yi amfani da wannan dama domin sanar da hukumar gudanawar kungiyar Wikki Tourists F.C game da shawarar da na yanke na yin murabus daga matsayina na babban mai horaswa (Technical Adviser) na kungiyar, tun daga 09/02/2026 “inji Maikaba

Wannan shawara ta zama dole ne sakamakon dalilai kamar haka:

Rashin hadin kai:
Akwai rashin jituwa tsakanin masu ruwa da tsaki na kungiyar, wanda hakan ke sanya wahalar cimma manyan burin na kungiyar da ta sanya a gaba.

Saboda tsaron lafiya na ina fuskanci
barazanar a yayin gudanar da aikina daga wasu bangarorin magoya bayan kungiyar, bisa yadda suke mun a fili da kuma ta kafafen sada zumunta inji shi.

Saboda wadannan dalilai, na ga ya dace in dauki matakin ajiye aiki bayan na nemi shawarar iyalina.

Ina kuma amfani da wannan dama domin gode wa hukumar gudanawar kungiyar bisa damar da suka bani nayin aiki a wannan babban kulob. Ina fatan za a karbi murabus dina.

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel
Next Post: Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shari’ar Abubakar Malami Ta Kaura Zuwa Sabon Alkali Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
  • Wike: Bazamuyi Sake Fubara Ya Sake Samun Nasara Ba Najeriya
  • Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika
  • Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.