Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina
Published: May 4, 2026 at 2:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Aƙalla mutane goma sha ɗaya sun rasa rayukansu bayan ‘yan bindiga sun kai harin ramuwar gayya a wasu ƙauyuka da ke Ƙaramar Hukumar Kankia a jihar Katsina Najeriya

Majiyoyi rawaito cewa rundunar ƴan sandan jihar ta bayyana cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 12 na rana a jiya Lahadi, inda maharan suka sake taruwa suka kai farmaki ƙauyukan Jeka da Kolo da Kwalgoro, suka buɗe wuta kan mazauna yankin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum 11 kafin jami’an tsaro su fatattake su.

Kwamishinan yan sandan jihar, CP Ali Umar Fagge, ya yi Allah-wadai da harin, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu. Ya kuma ba da umarnin a ƙaddamar da farautar masu laifin ta hanyar amfani da bayanan sirri domin cafke su.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya ce an ƙara yawan sintiri da aikin share dazuka domin gano maharan da suka tsere, tare da hana aukuwar irin wannan hari a gaba.

Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su kasance masu lura tare da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

A cewar ‘yan sanda, harin ramuwar gayyar ya biyo bayan nasarorin da jami’an tsaro suka samu a baya-bayan nan, ciki har da dakile satar shanu da kuma kwato dabbobi sama da 200, da kuma fatattakar wasu ‘yan bindiga a wani hari da suka kai.

Hakazalika, gwamnatin jihar Katsina ta yi tir da harin, tana mai cewa hari kan fararen hula aiki ne na ta’addanci. Ta kuma jaddada aniyar ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin al’umma da jami’an tsaro domin magance matsalar tsaro.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u
Next Post: ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
Farashin Man Fetur Yakara Tashi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Binne Gawar Tsohon Shugaban Sashen Hausa Na VOA, Leo Keyen Afrika
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi Afrika
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya Wasanni
  • Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
  • Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.