Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina
Published: May 4, 2026 at 2:03 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Aƙalla mutane goma sha ɗaya sun rasa rayukansu bayan ‘yan bindiga sun kai harin ramuwar gayya a wasu ƙauyuka da ke Ƙaramar Hukumar Kankia a jihar Katsina Najeriya

Majiyoyi rawaito cewa rundunar ƴan sandan jihar ta bayyana cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 12 na rana a jiya Lahadi, inda maharan suka sake taruwa suka kai farmaki ƙauyukan Jeka da Kolo da Kwalgoro, suka buɗe wuta kan mazauna yankin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum 11 kafin jami’an tsaro su fatattake su.

Kwamishinan yan sandan jihar, CP Ali Umar Fagge, ya yi Allah-wadai da harin, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu. Ya kuma ba da umarnin a ƙaddamar da farautar masu laifin ta hanyar amfani da bayanan sirri domin cafke su.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya ce an ƙara yawan sintiri da aikin share dazuka domin gano maharan da suka tsere, tare da hana aukuwar irin wannan hari a gaba.

Rundunar ta kuma buƙaci al’umma da su kasance masu lura tare da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro.

A cewar ‘yan sanda, harin ramuwar gayyar ya biyo bayan nasarorin da jami’an tsaro suka samu a baya-bayan nan, ciki har da dakile satar shanu da kuma kwato dabbobi sama da 200, da kuma fatattakar wasu ‘yan bindiga a wani hari da suka kai.

Hakazalika, gwamnatin jihar Katsina ta yi tir da harin, tana mai cewa hari kan fararen hula aiki ne na ta’addanci. Ta kuma jaddada aniyar ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin al’umma da jami’an tsaro domin magance matsalar tsaro.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u
Next Post: ‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
Wani Alkali A Kotun Amurka Ya Dakatar Da Kudurin Shugaba Trump Afrika
Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.