Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata
Published: February 14, 2026 at 3:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya yi watsi da zargin da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi masa dangane da bacewar Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata.

A wata sanarwa da tsohon Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida na Kano, Kwamared Muhammad Garba, ya sanya wa hannu, Ganduje ya bayyana zargin a matsayin mara tushe, tare da cewa yunƙuri ne na karkatar da alhakin abin da ya faru a jihar Kaduna kaɗai.

Sanarwar ta jaddada cewa Dadiyata ya rayu kuma ya gudanar da harkokinsa ne a Kaduna, inda aka san shi da sukar gwamnatin jihar a wancan lokaci.

A cewar sanarwar, babu wata hujja da ke nuna cewa ya fi mayar da hankali kan gwamnatin Kano ko kuma kan Ganduje.

Tsohon gwamnan ya buƙaci a yi nazari mai zurfi kan kalaman El-Rufai, yana mai cewa irin waɗannan manyan zarge-zarge ya kamata su kasance tare da hujjoji masu inganci, ba wai furucin siyasa kawai ba.

Ganduje ya kuma bayyana cewa jawo sunansa cikin lamarin ba tare da tabbatacciyar shaida ba na iya rikita jama’a kan batun da har yanzu bai samu cikakken bayani ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa a lokacin mulkinsa na wa’adi biyu a Kano, an san gwamnatin Ganduje da karɓar suka, hulɗa da kafafen yaɗa labarai, da kuma bai wa ’yan adawa damar bayyana ra’ayoyinsu ba tare da tsangwama ba.

Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa
Next Post: INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran Amurka
An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
  • ‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
  • Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.