Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya
Published: January 20, 2026 at 4:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya kammala ziyara ta biyu ta shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

Ziyarar ta gudana daga 4 zuwa 19 ga Janairu, 2026, inda aka mayar da hankali kan ƙarfafa tsare-tsaren aiki, da inganta haɗin gwiwa da hukumomin Saudiyya, tare da daidaita masu ba da hidima daga Najeriya da sauran masu ruwa da tsaki domin su dace da ka’idoji da jadawalin Saudiyya.

A sanarwar da Ahmad Muazu, mataimaki na musamman ga shugaban NAHCON kan yaɗa labarai ya fitar a ranar Talata, yayin ziyarar, tawagar NAHCON ta gana da manyan hukumomi, da suka haɗa da Ma’aikatar Hajji da Umrah, Hukumar Jiragen Sama (GACA), Ma’aikatar Lafiya, da masu kula da Mashā’ir, masauki da abinci, jiragen sama, da ‘yan Najeriya mazauna Saudiyya, da tsarin huldar kafafen yaɗa labarai.

Daga cikin manyan nasarorin da aka cimma; akwai kulla yarjejeniyoyin hidima, ɗora kwangiloli da jadawalin jirage a dandalin Nusuk Masar, duba asibitoci a Makkah da Madinah, tabbatar da ƙa’idar gwajin lafiya, da daidaita tsarin na’urorin dijital da aiki.

NAHCON ta kuma yi taro da hukumar kula da alhazai ta jihohi da kamfanonin yawon buɗe ido, domin ƙarfafa aiki a kan lokaci, ƙa’idoji da ingancin hidima kafin Hajjin 2026.

Hukumar ta ce yanzu za ta shiga mataki na gaba na shiri, ciki har da kammala kwangiloli, ɗora bayanan maniyyata, da ci gaba da haɗin gwiwa domin tabbatar da Hajji mai sauƙi kuma cikin tsari.

Labarai

Post navigation

Previous Post: CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya
Next Post: Tsohon Shugaban Kasa Obasanjo Ya Ziyarci IBB

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
  • Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.