Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya
Published: January 20, 2026 at 4:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Pakistan, ya kammala ziyara ta biyu ta shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

Ziyarar ta gudana daga 4 zuwa 19 ga Janairu, 2026, inda aka mayar da hankali kan ƙarfafa tsare-tsaren aiki, da inganta haɗin gwiwa da hukumomin Saudiyya, tare da daidaita masu ba da hidima daga Najeriya da sauran masu ruwa da tsaki domin su dace da ka’idoji da jadawalin Saudiyya.

A sanarwar da Ahmad Muazu, mataimaki na musamman ga shugaban NAHCON kan yaɗa labarai ya fitar a ranar Talata, yayin ziyarar, tawagar NAHCON ta gana da manyan hukumomi, da suka haɗa da Ma’aikatar Hajji da Umrah, Hukumar Jiragen Sama (GACA), Ma’aikatar Lafiya, da masu kula da Mashā’ir, masauki da abinci, jiragen sama, da ‘yan Najeriya mazauna Saudiyya, da tsarin huldar kafafen yaɗa labarai.

Daga cikin manyan nasarorin da aka cimma; akwai kulla yarjejeniyoyin hidima, ɗora kwangiloli da jadawalin jirage a dandalin Nusuk Masar, duba asibitoci a Makkah da Madinah, tabbatar da ƙa’idar gwajin lafiya, da daidaita tsarin na’urorin dijital da aiki.

NAHCON ta kuma yi taro da hukumar kula da alhazai ta jihohi da kamfanonin yawon buɗe ido, domin ƙarfafa aiki a kan lokaci, ƙa’idoji da ingancin hidima kafin Hajjin 2026.

Hukumar ta ce yanzu za ta shiga mataki na gaba na shiri, ciki har da kammala kwangiloli, ɗora bayanan maniyyata, da ci gaba da haɗin gwiwa domin tabbatar da Hajji mai sauƙi kuma cikin tsari.

Labarai

Post navigation

Previous Post: CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya
Next Post: Tsohon Shugaban Kasa Obasanjo Ya Ziyarci IBB

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
  • Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Dogarawan Ruwa Na Amurka Suna Yunkurin Shiga Wani jirgin Dakon Mai Da Aka Allakan Ta Da Venezuela Labarai
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.