Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya
Published: January 20, 2026 at 4:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Bankuna a Najeriya sun bayar da rahoton karuwar rashin biyan bashi a daga magidanta da kamfanoni duk da cewa samuwar rance da bukatar sa sun karu, a cewar binciken yanayin bashi na babban bankin Najeriya (CBN) na zangon karshe na 2025.

Rahoton ya nuna cewa rashin biyan bashi ya karu a dukkan nau’ikan rance, ciki har da rancen dake da jingina da wanda bai da jingina, da kuma na kamfanoni.

Kananan gidaje da kamfanoni kanana sun fi fuskantar matsala saboda hauhawar farashi, tsadar makamashi, da karancin kudin shiga.

A bangaren manyan kamfanoni, rashin biyan bashi ya kai kashi 6% a wasu lokuta, yayin da sauran kamfanonin kudi suka samu matsakaicin rashin biyan bashi na kashi 6.2%, lamarin da ke nuna tsanani a bangarorin tsarin kudi.

Duk da haka, bankuna sun kara bayar da rance ga gidaje da kamfanoni, amma babban bankin Najeriya ya yi gargaɗin cewa karuwar rashin biyan bashi na iya lalata ingancin kadarori da rage karfin bankuna.

CBN ta kuma ba da shawarar inganta tsarin dawo da bashi da kiyaye ka’idojin banki don rage matsalar.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas
Next Post: Hukumar NAHCON Ta Kamallah Shirye Shiryen Hajjin 2026 A Kasar Saudiya

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma Afrika
Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fiye Da Mutane 108 Sun Rasa Rayukansu A Ambaliyar Kenya Afrika
  • An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
  • Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai
  • Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
  • An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato Tsaro
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.