Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika

Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta
Published: April 23, 2026 at 7:43 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

​Rundunar sojin hadin gwiwa ta Operation Hadin Kai (OPHK) da ke lura da shiyya ta biyu a Najeriya ta yi nasarar fatattakar wani gagarumin hari da ’yan ta’adda suka kai yankin Kukareta a daren Laraba wayewar Alhamis.

​Harin, wanda aka fara shi jim kadan bayan tsakar dare zuwa misalin karfe 3:00 na asuba, ya gamu da tirjiya daga dakarun soji wadanda suka yi martani, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa bayan sun tafka asara mai yawa.
​
A cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba ya fitar a ranar 23 ga watan Afrilu, 2026, ya bayyana cewa sojoji sun yi nasarar kashe ’yan ta’adda 24 a yayin artabun.

​Haka kuma, binciken da sojoji suka gudanar a fagen daga bayan kura ta lafa ya kai ga gano dimbin makaman da ’yan ta’addan suka bari, wadanda suka hada da ​Bindigogi kirar AK-47 guda 18 da wasu manyan bindigogi na GPMG guda 3, ​Bindigogin kakkabo jiragen sama (PKT) guda 2 da bututun harba bama-bamai na RPG guda 3 da na Mortar guda 2, ​Guruneti (Hand grenades) guda 4 da kuma dimbin alburusai.

Sanarwar ta kara da cewa sojoji biyu ne suka samu raunuka a lokacin musayar wuta, kuma tuni aka duba lafiyarsu inda suke cikin yanayi mai kyau. Kazalika, wata motar yaki ta sojoji (Tank) guda daya ta samu matsala bayan tayoyinta sun fashe a lokacin da take kai dauki.

A halin yanzu, sojoji na ci gaba da bin sawun ’yan ta’addan da suka tsere da raunuka, inda aka ga alamun jini da kayayyakin magunguna a hanyoyin da suka bi yayin gudun ceton rai.

​Wannan nasara dai ta kara tabbatar da irin shirin da dakarun soji suke da shi na murkushe duk wani yunkuri na ’yan ta’adda a yankin Arewa maso Gabas, inda rundunar ta lashi takobin ci gaba da matsa lamba har sai ta kawo karshen ayyukan ta’addanci a yankin baki daya.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya
Next Post: Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro A Jihar Borno Sun Kama ‘Yan Bindiga Labarai
Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano Labarai
Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
Wasu Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Kwango Afrika
Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Likitoci Masu Neman Kwarewa Zasu Shiga Yakin Aiki
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
  • Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka
  • Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
  • Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.