Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro
Published: May 9, 2026 at 12:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasashen Najeriya da Amurka sun kulla yarjejeniyar kara zurfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, yaki da ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin Yammacin Afirka.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mai Taimakawa Shugaban Kasa kan Yada Labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Asabar, 9 ga watan Mayun 2026.

Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (NSA), Mallam Nuhu Ribadu, ya kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a Amurka, inda ya gana da manyan kusoshin gwamnatin kasar. A yayin ziyarar, Ribadu ya isar da sakon Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jajircewa wajen dorewar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Ribadu ya gana da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio da Sauran manyan jami’an diflomasiyya da na tsaro na kasar Amurka.

Babban makasudin wannan ganawa shi ne duba yadda za a inganta raba bayanan sirri da kuma karfafa ayyukan soji na hadin gwiwa. NSA Ribadu ya jaddada muhimmancin taimakon juna don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Sahel, musamman Ayukan ta’addanci da tsagera, Safarar miyagun kwayoyi da makamai da Laifukan da ake aikatawa ta hanyar yanar gizo.

Hukumomin Amurka sun jinjina wa Najeriya a matsayinta na jagora a yankin Afirka, musamman wajen jagorantar yaki da ta’addanci a tafkin Chadi.

A nata bangaren, Najeriya ta bayyana cewa tana amfani da dabarun karfin soja da kuma tattaunawa da inganta rayuwar jama’a don magance tushen matsalar rashin tsaro.

“Najeriya tana godiya ga Amurka bisa taimakon da take bayarwa a bangaren horar da jami’ai, ba da bayanan sirri, da kuma tallafin jinkai.” — Ribadu

A karshen taron, bangarorin biyu sun amince su ci gaba da tuntubar juna akai-akai ta hanyar hadin gwiwa na musamman don tabbatar da cewa dukkan yarjejeniyoyin da aka kulla sun fara aiki yadda ya kamata.

Afrika, Amurka, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP
Next Post: Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
‘Yan Sanda A Jihar Gombe Sun Karyata Kona Gidan Nafiu Bala Afrika
Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Majami’ar Anglican Zasuyi Taron Zaben Sabon Shugaba Afrika
  • Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar Amurka
  • Kasar Amurka Da Denmark Suna Rikici Akan Iyakar Greenland Amurka
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.