Kasashen Najeriya da Amurka sun kulla yarjejeniyar kara zurfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, yaki da ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin Yammacin Afirka.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mai Taimakawa Shugaban Kasa kan Yada Labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Asabar, 9 ga watan Mayun 2026.
Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (NSA), Mallam Nuhu Ribadu, ya kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a Amurka, inda ya gana da manyan kusoshin gwamnatin kasar. A yayin ziyarar, Ribadu ya isar da sakon Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jajircewa wajen dorewar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.
Ribadu ya gana da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio da Sauran manyan jami’an diflomasiyya da na tsaro na kasar Amurka.
Babban makasudin wannan ganawa shi ne duba yadda za a inganta raba bayanan sirri da kuma karfafa ayyukan soji na hadin gwiwa. NSA Ribadu ya jaddada muhimmancin taimakon juna don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Sahel, musamman Ayukan ta’addanci da tsagera, Safarar miyagun kwayoyi da makamai da Laifukan da ake aikatawa ta hanyar yanar gizo.
Hukumomin Amurka sun jinjina wa Najeriya a matsayinta na jagora a yankin Afirka, musamman wajen jagorantar yaki da ta’addanci a tafkin Chadi.
A nata bangaren, Najeriya ta bayyana cewa tana amfani da dabarun karfin soja da kuma tattaunawa da inganta rayuwar jama’a don magance tushen matsalar rashin tsaro.
“Najeriya tana godiya ga Amurka bisa taimakon da take bayarwa a bangaren horar da jami’ai, ba da bayanan sirri, da kuma tallafin jinkai.” — Ribadu
A karshen taron, bangarorin biyu sun amince su ci gaba da tuntubar juna akai-akai ta hanyar hadin gwiwa na musamman don tabbatar da cewa dukkan yarjejeniyoyin da aka kulla sun fara aiki yadda ya kamata.


