Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro
Published: May 9, 2026 at 12:56 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kasashen Najeriya da Amurka sun kulla yarjejeniyar kara zurfafa hadin gwiwa a fannin tsaro, yaki da ta’addanci da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin Yammacin Afirka.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Mai Taimakawa Shugaban Kasa kan Yada Labarai, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Asabar, 9 ga watan Mayun 2026.

Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (NSA), Mallam Nuhu Ribadu, ya kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a Amurka, inda ya gana da manyan kusoshin gwamnatin kasar. A yayin ziyarar, Ribadu ya isar da sakon Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jajircewa wajen dorewar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

Ribadu ya gana da Mataimakin Shugaban Amurka, J.D. Vance, Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Marco Rubio da Sauran manyan jami’an diflomasiyya da na tsaro na kasar Amurka.

Babban makasudin wannan ganawa shi ne duba yadda za a inganta raba bayanan sirri da kuma karfafa ayyukan soji na hadin gwiwa. NSA Ribadu ya jaddada muhimmancin taimakon juna don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Sahel, musamman Ayukan ta’addanci da tsagera, Safarar miyagun kwayoyi da makamai da Laifukan da ake aikatawa ta hanyar yanar gizo.

Hukumomin Amurka sun jinjina wa Najeriya a matsayinta na jagora a yankin Afirka, musamman wajen jagorantar yaki da ta’addanci a tafkin Chadi.

A nata bangaren, Najeriya ta bayyana cewa tana amfani da dabarun karfin soja da kuma tattaunawa da inganta rayuwar jama’a don magance tushen matsalar rashin tsaro.

“Najeriya tana godiya ga Amurka bisa taimakon da take bayarwa a bangaren horar da jami’ai, ba da bayanan sirri, da kuma tallafin jinkai.” — Ribadu

A karshen taron, bangarorin biyu sun amince su ci gaba da tuntubar juna akai-akai ta hanyar hadin gwiwa na musamman don tabbatar da cewa dukkan yarjejeniyoyin da aka kulla sun fara aiki yadda ya kamata.

Afrika, Amurka, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP
Next Post: Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ

Karin Labarai Masu Alaka

Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
NSCIA Ta Gargadi Gwamnati Kan Zargin Tauye Haƙƙin Musulmi Afrika
An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza Labarai
  • Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
  • Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kamaru Ta Lallasa Malawi 3-0, Ta Lashe Kofin WAFCON Na Farko A Tarihi Wasanni
  • Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.